Tsaka mai wuyar da Amurka ke ciki kan ko za ta tallafa wa Isra’ila wajen kai wa Iran hari, ko kuma ta tsame hannunta kacokan daga rikicin ya fallasa rarrabuwar kawunan da ke tsakanin masu goyon bayan shugaba Donald Trump.
Rahotanni sun nuna cewa shugaban na Amurka na tunanin tallafa wa Iran wajen tarwatsa cibiyoyin sarrafa nukiliya na Iran, bayan tattaunawar da ya yi da masu ba shi shawara kan tsaro a fadar White House, ranar Talata.
Masu goyon bayan taken Trump na ‘fifita Amurka a kowane yanayi’ sun dage kan cewa Trump ya ci alwashin kauce wa tsoma Amurka cikin “dagayen yaƙe-yaƙe” irin waɗanda suka janyo kashe-kashen ɗimbin dakarun Amurka a Afghanistan da Iraqi.
Sai dai ƴan ina-da-yaƙi na jam’iyyar Republican mai mulki na ingiza Trump ya afka wa Iran.
Sanata daga Kudancin Carolina, Lindsey Graham ya ce abu ne da zai amfani Amurka idan aka hana Iran mallakar makamin nukiliya.
Iran dai ta dage kan cewa shirinta na nukiliya na zaman lafiya ne.










