Daga Hassan Umar Gwammaja
Ɗaya daga cikin ‘ya’yan marigayi Manjo Janar Abubakar Rabe mai ritaya, Isyaka Rabe, ya musanta ikirarin da gwamnatin Jihar Katsina ta yi cewa mahaifinsa ya rasu ne sakamakon matsalolin ciwon sukari da hawan jini.
A wata hira da ya yi da Deutsche Welle (DW), Isyaka ya ce mahaifinsa bai taɓa fama da ciwon sukari ko hawan jini ba. Ya bayyana cewa wasu na zargin wataƙila ya mutu ne bayan maciji ya sare shi, bisa ga wani bidiyo na ƙarshe da masu garkuwa da shi suka fitar, amma ya ce Allah kaɗai ne ya san ainihin musabbabin mutuwarsa.
Ya bayyana marigayin a matsayin mutum mai ibada, son zaman lafiya da rayuwa mai sauƙi, yana mai cewa ya mutu a matsayin jarumi.
Isyaka ya kuma ce bai san yadda aka karɓo gawar mahaifinsa ba, yana mai cewa gwamnati ce kaɗai za ta iya yin bayani kan hakan.
Haka kuma ya ƙaryata rahotannin da ke yawo a kafafen sada zumunta cewa mahaifiyarsa, wadda aka sace tare da mahaifinsa, ta samu ‘yanci, yana mai tabbatar da cewa har yanzu tana hannun masu garkuwa da mutane.
A nata ɓangaren, ɗiyar marigayin, Adda Abubakar, ta wallafa a shafinta na X cewa mahaifinta bai da ciwon sukari, tana mai jaddada cewa cizon maciji ne ya yi sanadin mutuwarsa.
An sace Janar Rabe da matarsa ne a ranar 30 ga Mayu, 2026, a kan hanyar Marabar Musawa zuwa Kafinsoli da ke Ƙaramar Hukumar Matazu ta Jihar Katsina. Daga bisani ya rasu yana tsare a hannun masu garkuwa da shi.
Sai dai gwamnatin Jihar Katsina ta ce marigayin ya mutu ne sakamakon matsalolin ciwon sukari da hawan jini, yayin da iyalansa da wasu majiyoyi ke cewa cizon maciji ne ya yi ajalinsa.












