Shugabancin Kungiyar matuka manyan motocin Tifa na jihar Kano ya bayyana gudunmawar da yake baiwa Gwamnatin a matsayin wadanda Gwamnati ya kamata ta kallesu domin Samar musu gurin tsayawa na din-din-din a kwaryar jihar Kano.
Shugaban Kungiyar kwamared Shafi’i Ibrahim zainawa ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da Manama labarai a ofishin Kungiyar dake nan Kano.
Shafi’i Ibrahim yace, Kungiyar masu tukin motocin Tifa suna mutukar baiwa Gwamnatin jihar Kano cikakken hadin Kan daya kamata, musamman abubuwan da suka shafi bangaren tuki, Inda yace akwai bukatar Gwamnati ta rika sanya Kungiyar a cikin Al”amuranta da zai Kara habaka Kungiyar da alummar jihar Kano.
Yace, akwai bukatar Gwamnati ta rika baiwa ‘ya’yan Kungiyar kwangila a duk lokacin da ta tashi baiwa wasu kamfanoni kwangila ta kwashe yashi da sauran aikace -aikace da gyare -gyaren hanyoyi a fadin jihar Kano.
Shugaban Kungiyar yace, akwai alkawarirrika da dama da Gwamnatin jihar Kano ta yiwa Kungiyar,a lokacin Baya a don haka Kungiyar take Kira ga Gwamnan da ya tuna da Kungiyar duba da halin da ta samu kanta a ciki.
Yace lokaci yayi da Gwamnatin jihar Kano za ta tallafawa “ya”yanta da tallafi Wanda za su ci gaba da bayyana ayyukan Gwamnatin Yadda ya domin ciyar da Jihar Kano gaba.
Shugaban Kungiyar yace, babbar matsalar su rashin gurin tsayawa na din-din-din da za su rika tsayawa domin su yi gogayya da sauran kungiyoyin matuka manyan motocin Tifa na sauran jihohi da suke a fadin kasar nan.
Daga karshe Shugaban Kungiyar yayi Kira ga dukkannin ‘ya’yan Kungiyar da su ci gaba da baiwa Gwamnatin jihar Kano da Kungiyar cikakken hadin Kan daya kamata domin ciyar da alummar jihar gaba.
COV/ISGAMA/











Aluminium Fabrication installation