Wani matashi mai suna Abdul’azi Dan Asalin Unguwa Uku, mazaunin Ƙaramar Hukumar Garun-Malam ta Jihar Kano, ya jikkata wata dattijuwa mai suna Hajiya Sahura Kura, mai kimanin shekaru 75, tare da yi mata barin makauniya.
Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne bayan dattijuwar ta hana matashin shiga ɗakin karɓar haihuwa, bisa dokar da ta hana maza shiga sashen kula da mata masu haihuwa.
Hajiya Sahura ta shafe kimanin shekaru 35 tana aiki a sashen kula da mata masu karɓar haihuwa a Babban Asibitin Ƙaramar Hukumar Kura. Mahukuntan asibitin sun kama wanda ake zargin a lokacin da yake ƙoƙarin ci gaba da dukan dattijuwar.
Shugaban asibitin, Dr. Muktar Wudil, ya umarci sakataren asibitin, Aliyu Isma’ila Kiru, da ya miƙa wanda ake zargin ga rundunar ’yan sandan Kura domin gudanar da bincike.
Bayan kammala bincike, ’yan sandan sun gurfanar da Abdul’azi a gaban Kotun Majistare ta Ƙaramar Hukumar Kura, ƙarƙashin jagorancin Chief Magistrate Muhammad Alhaji Isa. Mai gabatar da ƙara, Inspector Nasiru Abubakar Dansakkwato, ya gabatar da takardar tuhuma a gaban kotun.
Bayan an karanta masa tuhumar, alkalin kotun ya tambaye shi ko ya aikata laifin, inda wanda ake zargin ya amsa cewa ya aikata laifin.
Alkalin ya yi masa nasiha tare da tunasar da shi irin shekarun dattijuwar da kuma tsawon lokacin da ta shafe tana yi wa al’umma hidima. Sai dai saboda ƙarancin lokaci da kuma halin da wanda abin ya shafa ke ciki, kotun ta ɗage sauraron shari’ar zuwa 17 ga Satumba, 2026.
Kotun ta kuma bayar da umarnin tsare wanda ake zargin a hannun jami’in gidan yari da gyaran hali, Hasan Muhammad Gambo Gwaneri, har zuwa ranar ci gaba da sauraron shari’ar.










