Daga Hassan Umar Gwammaja
Waton Kungiyar Twins Empowerment Initiative Kano ta mika godiya ta musamman ga Mai girma Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, bisa irin goyon bayan da ya bayar wajen tabbatar da cewa tagwayen da aka raba su a kasar Saudiyya za su ci gaba da samun kulawa ta musamman da kuma daukar nauyin karatunsu har zuwa matakin jami’a.
Shugaban ƙungiyar, Malam Hassan Magashi, tare da Sakataren ƙungiyar, Malam Hassan Kabara, sun bayyana farin cikinsu da godiyarsu bisa wannan alkawari, wanda ya nuna jajircewar gwamnatin Kano wajen tallafawa yara musamman tagwaye da kuma kare martabarsu.
Kungiyar ta kuma mika godiya ga gidauniyar Sarki Salman bin Abdul’aziz Al Saud da kuma ofishin jakadancin Saudiyya a Najeriya, bisa daukar nauyin aikin raba tagwayen da kuma kyakkyawar kulawar da aka basu tsawon shekaru biyu a ƙasar mai tsarki.
A cewar kungiyar, wannan aiki ya zama abin tarihi da kuma hujja ta alheri ga iyayen tagwayen, al’ummar Kano, da kuma Najeriya baki ɗaya. Twins Empowerment Initiative Kano ta sha alwashin ci gaba da mara baya da irin wadannan shirye-shirye da kuma kare muradun tagwaye a cikin al’umma.
Ƙungiyar ta roki Allah ya saka da alheri ga Mai girma Gwamna Abba Kabir Yusuf, ga gwamnatin Saudiyya, da duk masu ruwa da tsaki da suka bayar da gudunmawa wajen ganin wannan aiki mai albarka ya tabbata cikin nasara. Shugaban Ƙungiya









