Kotun Majistare da ke Kwanar Dangora, a ƙaramar hukumar Bebeji ta Jihar Kano, ta yanke wa wata matar aure mai suna Maimuna hukunci bayan samunta da laifin watsa tafasasshen ruwa ga kishiyarta, Zainabu.
Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne a unguwar Rimi Bakin Kwata da ke Kwanar Dangora, inda ake zargin Maimuna ta kai wa sabuwar amaryar harin sakamakon rikicin cikin gida da ake dangantawa da kishi. An ce Zainabu ta samu munanan ƙonewa a sassan jikinta, lamarin da ya sa makwabta suka garzaya domin kai mata ɗauki kafin a kai ta asibiti.
A gaban kotu, ɗan sanda mai gabatar da ƙara, Sajan Aminu Muhammad Ciromawa, ya gabatar da takardar tuhuma tare da shaidu da suka haɗa da rahoton asibiti da takardun magunguna. A zaman farko, wacce ake zargi ta amsa laifin da ake tuhumarta da shi.
Sai dai a zaman da aka koma domin ci gaba da shari’ar, Maimuna ta samu lauya, Barista Ibrahim Salihu Faki, wanda ya nemi a sake karanta mata tuhumar. Bayan an sake karanta ta, Maimuna ta musanta aikata laifin, yayin da lauyanta ya nemi a ba ta beli. Sai dai mai gabatar da ƙara ya roƙi kotu ta yi hukunci bisa amsar laifin da ta yi tun farko.
Bayan nazarin hujjoji da takardun asibiti, Babban Alƙalin Kotun, Chief Majistare Muhammad Alh. Isa, ya yanke wa Maimuna hukuncin zaman watanni huɗu a gidan gyaran hali ba tare da zaɓin tara ba. Haka kuma, kotun ta ci ta tarar naira dubu ɗari takwas da arba’in. Idan ta gaza biya, za ta ƙara yin shekara biyu a gidan gyaran hali.
Alƙalin ya bayyana cewa tana da damar ɗaukaka ƙara cikin wa’adin wata guda. Bayan kammala shari’ar, jami’an gidan gyaran hali suka karɓi wacce aka yankewa hukuncin domin aiwatar da umarnin kotu.
A nasa ɓangaren, lauyan wacce aka yankewa hukunci, Barista Ibrahim Salihu Faki, ya shaida wa manema labarai cewa za su ɗaukaka ƙara kan hukuncin da kotun ta yanke.









