Abuja – Yayin da labarin murabus ɗin shugaban APC na ƙasa, Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya karaɗe Najeriya, an hangi jagoran NNPP, Rabiu Musa Kwankwaso a Abuja.
Tsohon ɗan takarar shugaban kasa, Dr. Rabiu Musa Kwankwaso ya kaddamar da babban ofishin jam’iyyar NNPP a babban birnin tarayya Abuja a yau Juma’a.
Mai taimakawa Kwankwaso kan harkokin midiya, Hon. Saifullahi Hassan ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X.
Sanarwar ta ce jagoran NNPP ya kaddamar da babban ofishin jam’iyyar reshen Abuja a unguwar Wuse Zone 6.
Taron ya samu halartar manyan ƙusoshin jam’iyyar ciki har da shugaban NNPP na ƙasa, Dr. Ahmed Ajuji da sauran ƴan kwamitin gudarwa (NWC) da magoya baya.












