Ma’aikatar Harkokin Wajen Ƙasar China ta tabbatar a ranar Laraba cewa za a gudanar da tattaunawar ƙasashe uku tsakanin China, Pakistan da Afghanistan a birnin Ürümqi, wanda shi ne babban birnin yankin Xinjiang da ke arewa maso yammacin China.
Taron zai haɗa wakilai daga hukumomin gwamnati masu kula da harkokin diflomasiyya, da tsaro da kuma kare ƙasa, kuma za a gudanar da shi Kamar yadda aka tsara.










