Majalisar Dokokin Jihar Kano a ranar Alhamis ta gudanar da tantancewa ga wanda aka nada a matsayin mataimakin gwamna, Murtala Sule Garo, bayan wata takardar bukata daga Gwamna Abba Kabir Yusuf domin neman amincewar majalisar.
Da yake zantawa a wata hira ta musamman da SolaceBase, Babban Sakataren Yaɗa Labarai na Majalisar kuma mai magana da yawun Kakakin Majalisar, Kamaluddin Sani Shawai, ya bayyana cewa an fara wannan tsari ne bayan gwamnan jihar ya aike da bukata a hukumance ga majalisar domin tantance dan takarar.
Shawai ya kara da cewa nan take bayan karbar bukatar gwamnan, Kakakin Majalisar, Jibril Ismail Falgore, ya kafa kwamiti mai mambobi 12 karkashin jagorancin Mataimakin Kakakin Majalisar, Bello Muhammad Butubutua, domin gudanar da aikin cikin gaggawa.











