• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Atiku, Kwankwaso , Obi Sun Jagoranci Zanga-Zanga A Babban Birnin Tarayya Abuja

aksam by aksam
April 8, 2026
Reading Time: 2 mins read
0
Home SIYASA
ADVERTISEMENT
472
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

RelatedPosts

Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, Ya Koma Jam’iyyar National Democratic Congress (NDC) A Hukumance; Inda Ya Karɓi Katin Zama Mamba Na Jam’iyyar

Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Mohammed Ya Fice Daga Jam’iyar PDP

Wasu Dalilin Da Suka Sa Kwankwaso Ke Shirin Ficewa Daga Jam’iyyar ADC

  Daga: Hassan Umar Gwammaja

Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Atiku Abubakar, tare da wasu fitattun jiga-jigan jam’iyyar ADC, sun gudanar da zanga-zanga zuwa hedikwatar Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) da ke Abuja, domin nuna rashin jin dadinsu kan abin da suka bayyana a matsayin tauye hakkinsu a cikin jam’iyyar.

Masu zanga-zangar sun zargi shugabancin INEC da katsalandan da kuma nuna rashin adalci, wanda suka ce na hana wasu bangarori gudanar da harkokinsu yadda ya kamata a cikin ADC.

Da yake jawabi, Atiku Abubakar ya bayyana cewa zuwansu INEC na da nufin neman hukumar ta sa baki, tare da tabbatar da cewa ana bin doka da ka’idojin jam’iyya wajen tafiyar da harkokinta.

Ya kuma gargadi cewa idan ba a dauki matakin gaggawa ba, rikicin na iya haifar da illa ga dimokuradiyya da kuma hadin kan ‘yan siyasa a Najeriya.

Masu zanga-zangar sun bukaci INEC da ta gudanar da cikakken bincike kan rikicin da ke addabar jam’iyyar ADC, tare da daukar matakan da suka dace domin dawo da zaman lafiya da adalci.

A yayin zanga-zangar, jami’an tsaro sun bazu a wurin domin tabbatar da zaman lafiya, inda aka gudanar da komai cikin lumana ba tare da wata hatsaniya ba.

Majalisa ta sanar da matsayarta ta karshe kan batun zarge-zargen da take yi wa tsohon mataimakin gwamnan Kano

Wannan mataki na zuwa ne a daidai lokacin da rikici ke kara kamari tsakanin bangarori daban-daban na jam’iyyar ADC, lamarin da ke ci gaba da janyo cece-kuce a fagen siyasar kasar nan.

Rahotanni sun nuna cewa rikicin shugabanci a jam’iyyar na gaban kotu, yayin da ake ci gaba da samun sabani a tsakanin mambobinta.

Daga cikin wadanda suka halarci zanga-zangar akwai Rabiu Musa Kwankwaso, Aminu Waziri Tambuwal, Peter Obi, Rauf Aregbesola da kuma Dino Melaye, tare da sauran jiga-jigan siyasa.

Share189Tweet118SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

China ta ci Alwashin Cimma matsaya a yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin Amurka da Iran

Next Post

Ma’aikatar harkokin wajen China ta magantu kan tattaunawar sulhu tsakanin Pakistan da Afghanistan

aksam

aksam

RelatedPosts

Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, Ya Koma  Jam’iyyar National Democratic Congress (NDC)  A Hukumance; Inda Ya Karɓi Katin Zama Mamba Na Jam’iyyar
SIYASA

Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, Ya Koma Jam’iyyar National Democratic Congress (NDC) A Hukumance; Inda Ya Karɓi Katin Zama Mamba Na Jam’iyyar

by aksam
May 3, 2026
Gwamnatin Jihar Bauchi Ta Umarci  Duk Masu Riƙe Da Mukaman Siyasa Dake Da Niyyar Tsayawa Takara Dasu Yi Murabus Kafin Ranar Juma’a 24 ga Watan Afrilu 2026
SIYASA

Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Mohammed Ya Fice Daga Jam’iyar PDP

by aksam
May 2, 2026
Ba Za Mu Bawa Kwankwaso Tikitin Takarar Shugabancin Kasa A Jam’iyyarmu— NNPP
SIYASA

Wasu Dalilin Da Suka Sa Kwankwaso Ke Shirin Ficewa Daga Jam’iyyar ADC

by aksam
May 2, 2026
Masu Ruwa Da Tsaki A  APCn Kano Sun Amince Da Takarar Abba da Tinubu Karo Na Biyu A Zaɓen 2027
SIYASA

Masu Ruwa Da Tsaki A APCn Kano Sun Amince Da Takarar Abba da Tinubu Karo Na Biyu A Zaɓen 2027

by aksam
May 1, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Vertrauenswürdige Quellen und Transparenz in der Online-Casino-Branche: Ein Schlüssel für nachhaltigen Erfolg

April 21, 2025
Wasu Yan jam’iyar APC na nuna kosawar su da jagorancin Ganduje

Wasu Yan jam’iyar APC na nuna kosawar su da jagorancin Ganduje

January 21, 2024
ADVERTISEMENT

Trending.

Mu Na Gayyatar  ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Comr.  Usaini Sani Adamu !!!

Mu Na Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Comr. Usaini Sani Adamu !!!

April 24, 2026
Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Umar SA’ID

Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Umar SA’ID

April 20, 2026
Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

May 4, 2026
Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID

Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID

April 17, 2026
Atiku, Kwankwaso , Obi Sun Jagoranci Zanga-Zanga A Babban Birnin Tarayya Abuja

Atiku, Kwankwaso , Obi Sun Jagoranci Zanga-Zanga A Babban Birnin Tarayya Abuja

April 8, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media