Daga Hassan Umar Gwammaja
Tsohon gwamnan Kano Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya na ta shirye-shiryen barin jam’iyyar ADC zuwa jam’iyyar NDC.
Aksam Media ta hadu wasu dalilai daban-daban da ake ganin su ne suke kokarin baiwa Kwankwaso damar ficewa daga jam’iyyar ta ADC da a yanzu haka bai wuce kwanaki 33 da komawa cikinta.
Akwai wasu Rahotanni da ke cewa Kwankwaso na son komawa NDC ne saboda kokarin da aka ce Tsohon shugaban Kasa Obasanjo na yunkurin hada kwankwaso da Peter Obi takarar shugaban Kasa a jam’iyyar a zaɓen 2027.
Amma a wata hira da aka yi da makusancin Kwankwaso Shehu Wada Sagagi ya ce yawan tarin shari’un jam’iyyar ADC dake gaban kotuna ne yasa dole su fice daga jam’iyyar domin gudun matsala bayan zabe.
Shehu Wada ya ce Karin Kan wancan dalilin har da bukatar da gwamnatin tarayya ta mikawa INEC na neman a rushe jam’iyyar ta ADC saboda a zaɓen da ya gabata ba ta sami Nasarar lashe zaben ko da na Dan majalisa ba ne.
Ya ce dole ne su nemi mafita domin Kalubalantar jam’iyyar APC wacca ta Kasa kamarwa yan Kasa abubuwan da suke bukata.
Yusuf Kofar mata shi ma wani Babban hadimi ne a gidan kwankwaso shi ma ya bayyana wasu dalilai da ya ce sun ishe su dalilin ficewa daga jam’iyyar ADC.
Ya bayyana cewa jam’iyyar ADC na fuskantar manyan kalubale na cikin gida da na waje da ka iya kawo cikas ga hadin kanta da kuma ci gabanta a matsayin jam’iyyar adawa.
“Duk da hukuncin Kotun Koli da ya yi wa jam’iyyar ADC gata a shari’ar da ta shafi Nafi’u Bala, akwai barazana a ci gaba da daukar hakan a matsayin cikakkiyar nasara. Rahotanni sun nuna cewa Kotun Kolin ta soke umarnin ci gaba da zaman yadda ake ciki ne kawai, yayin da shari’ar asali ke ci gaba a Babbar Kotun Tarayya, lamarin da ke haifar da fargaba kan abin da zai biyo baya”.
Haka zalika, Kofarmata ya ce kwanan nan wata Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta soke zabukan cikin gida da kuma babban taron jam’iyyar na kasa, matakin da ke kara jefa jam’iyyar cikin wani sabon rudani na shari’a wanda ke bukatar daukar matakin gaggawa.
“A jihar Kano ma, wani bangare na jam’iyyar ya shigar da kara a Babbar Kotun Jiha, inda kotun ta dage sauraron shari’ar na tsawon wata guda. Bugu da kari, bangaren ya sake shigar da wata kara a Babbar Kotun Tarayya da ke Kano, yana neman a dakatar da shugabannin jam’iyyar na jiha daga gudanar da duk wani aiki, ciki har da zaben fidda gwani, inda ake sa ran fara sauraron karar nan ba da jimawa ba”. Inji Yusuf Kofarmata
Ya kara da cewa A gefe guda kuma, an rawaito cewa shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ya gargadi jam’iyyar ADC da ta yi taka-tsantsan domin kaucewa irin abin da ya faru da jam’iyyar APC a jihar Zamfara a shekarar 2019, lokacin da ta rasa dukkan kujerunta sakamakon hukuncin kotu. Sai dai wasu na ganin wannan gargadi na iya kara dagula al’amura maimakon rage su.
Kofar mata ya ce ana zargin gwamnatin APC karkashin jagorancin Bola Ahmed Tinubu da hannu wajen haddasa yawancin rikice-rikicen da ke addabar jam’iyyun adawa, zargin da ke kara jawo cece-kuce a fagen siyasa.
Dangane da haka, masu sharhi na kira ga dukkan masu ruwa da tsaki da su yi zurfin tunani kan wadannan matsaloli tare da nemo mafita mai dorewa domin tabbatar da cewa jam’iyyar ADC ta samu damar shiga zaben shekarar 2027 ba tare da tangarda ba.
Baya ga wadannan dalilai da Kofar mata ya bayan, Muna daf da kammala hada Wannan rahoton Jaridar Aksam Media ta ci karo da wani rahoto na Jaridar The Cable da ke cewa Kwankwaso da Peter Obi za su koma jam’iyyar NDC a mako mai zuwa.
Hakan dai na kunshe ne cikin wata sanarwa da kakakin kungiyar Kwankwasiyya Habibu Sale mailemo ya fitar .












