Al’ummar Maza’bar Kubaraci Da Tsauni da Kasuwar Gemu daFulatan a Karamar Hukumar Madobi Sun Futo Zanga-Zangar Lumana Domin Bayyana Korafe-Korafen’su tare da Kira Zuwa Ga ‘DanMajalisarsu
Na Tarayya Hon Yusif Umar Datti Da Sanantan Kano ta Tsakiya Hon Rufai Sani Hanga Dana Jaha Maiwakiltar Karamar Hukumar Mabodobi Hon Suleman Muktar Da Mai-Girma Gwamnan Jahar Kano Injiniya Abba Kabir Yusif domin fama da rashin kayan More rayuwa da Suke fama da shi a Yankin su
Yayin Ganawarsu Da Manema Labarai Ciki Harda Wakilin Aksammedia Dantala Uba Nuhu Kura Sun Bayyana suna Fuskantar Rashin Wutar Lantarki sun ce sama da shekaru 20 aka Samarwa Alummar Yankin Turakun Wutar Lantarki Amma har Yanzu an Gaza Samar musu da wutar
Rashin Samuwar Wutar Lantarkin ya sa Su ka yi Ta Bibiyar ‘Yan-Majalisun’su Daban-Daban ta hanyar Rubuta Masu Wasikun Neman Cigaban Aikin Saka Masu Wutar Lantarkin
Sannan sun Mika rokonsu Ga Gwamnatim Jahar Kano tare Da Yiwa Gwamnan Jahar Kano
Tuni Kan Halin Da Suke Ciki Na Matsalar’ Wutar Lantarki a Yankunan’su.
A karshe Al’ummar sun Roki Mai-Girma Gwamnan Jihar Kano Tare Da Yi Masa Tuni Kan Halin Da Al’ummar Yan-Kunan Ke Ciki Na Rashin Wutar Lantarkin Damin ya Share Masu Hawayensu












