Daga Hassan Umar Gwammaja
A yayin Wani taron siyasa a Ƙaramar Hukumar Ungogo Dake Jihar inda wasu fusatattun matasa sun kona fastocin ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NDC, Peter Obi, da abokin takararsa, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso.
Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne a dai-dai lokacin da ake gudanar da harkokin yaɗa manufofin jam’iyyar a yankin, inda aka ce fusatattun matasa sun lalata kayayyakin yaƙin neman zaɓen jam’iyyar tare da ƙona fastocin jagororinta.
Gwamnan Jigawa Ya Dakatar Da Hadimansa Guda 4
Wani bidiyo da ya karade kafafen sada zumunta ya nuna yadda shima shugaban jam’iyyar NDC na Ƙaramar Hukumar Ungogo, Bilyaminu Bachirawa, aka janyoshi daga kan babur yayin da rikicin.
Wannan lamari na zuwa ne kwanaki kaɗan bayan jam’iyyar NDC ta tabbatar da Peter Obi a matsayin ɗan takararta na shugaban ƙasa, tare da ayyana Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso a matsayin abokin takararsa gabanin zaɓen shekarar 2027.
Ya zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, hukumomin tsaro ba su fitar da wata sanarwa a hukumance kan abin da ya faru ba. Haka kuma, shugabannin jam’iyyar NDC a matakin jiha da na ƙasa ba su yi martani kan lamarin ba. Kano City Guide
Sai dai masu ruwa da tsaki na ci gaba da kira ga magoya bayan jam’iyyun siyasa da su guji tayar da zaune tsaye tare da rungumar zaman lafiya domin tabbatar da an gudanar da harkokin siyasa cikin kwanciyar hankali da mutunta ra’ayin juna.












