• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

aksam by aksam
May 4, 2026
Reading Time: 1 min read
0
Home LABARAI
ADVERTISEMENT
483
SHARES
1.6k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Daga: Hassan Umar Gwammaja

A yau Litinin, 4 ga watan Mayu, 2026, an cika shekaru 24 cif da aukuwar mummunan hatsarin jirgin sama a unguwar Gwammaja da ke birnin Kano—ɗaya daga cikin mafi muni a tarihin sufurin jiragen sama a Najeriya.

RelatedPosts

Sarkin Zurmi Ya Rasu Bayan Shekaru Biyar A Kan Sarauta

Irin Yadda Aka Gudanar Da Zagayen Mauludn Tunawa Ga Ranar Da Aka Haifi Annabi Muhammadu SWA A Garin Nkawkawo

Kano State Govt ends 50 year BUK/Rimin zakara Land Dispute

Hatsarin ya faru ne a ranar 4 ga Mayu, 2002, lokacin da wani jirgi mai ɗauke da tagwayen inji ƙirar BAC 1-11-500, wanda aka ƙera a ƙasar Birtaniya, ya yi hatsari jim kaɗan bayan tashinsa daga filin jirgin sama na Kano, yayin da yake kan hanyarsa ta zuwa jihar Legas.

Rahotanni sun nuna cewa akalla mutane 148 ne suka rasa rayukansu a hatsarin, yayin da wasu 51 suka jikkata. Daga cikin waɗanda hatsarin ya rutsa da su har da Ministan Wasanni na wancan lokaci, Ishaya Mark Aku, wanda ke kan hanyarsa ta zuwa Legas domin kallon wasan sada zumunta tsakanin ƙasashen Najeriya da Kenya.

Kamfanin jirgin, EAS Airlines, ya bayyana cewa mutum huɗu ne kawai suka tsira daga hatsarin, ciki har da fasinjoji uku da kuma ma’aikacin jirgin guda ɗaya.

Masana sun bayyana wannan hatsari a matsayin ɗaya daga cikin mafi muni a tarihin jiragen sama a ƙasar nan, sakamakon yawan asarar rayuka da dukiyoyi da ya haifar.

Lamarin ya kuma haifar da ƙara mai da hankali kan tsaurara matakan tsaro da inganta kula da harkokin sufurin jiragen sama a Najeriya.

Share193Tweet121SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

NDLEA Ta Kama Mutane 6, Ta Rushe Maboyar Miyagun Kwayoyi a BUK Old Site Kano

Next Post

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Ya Sanya Ranar Talata 05 GA watan Mayu 2026, A Matsayin Ranar Da Zai Jagoranci Rantsar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan

aksam

aksam

RelatedPosts

Sarkin Zurmi Ya Rasu Bayan Shekaru Biyar A Kan Sarauta
LABARAI

Sarkin Zurmi Ya Rasu Bayan Shekaru Biyar A Kan Sarauta

by Khadija Maitaya
September 1, 2026
Irin Yadda Aka Gudanar Da Zagayen Mauludn Tunawa Ga Ranar Da Aka Haifi  Annabi Muhammadu SWA  A Garin Nkawkawo
Uncategorized

Irin Yadda Aka Gudanar Da Zagayen Mauludn Tunawa Ga Ranar Da Aka Haifi Annabi Muhammadu SWA A Garin Nkawkawo

by aksam
September 1, 2026
Kano State Govt ends 50 year BUK/Rimin zakara Land Dispute
LABARAI

Kano State Govt ends 50 year BUK/Rimin zakara Land Dispute

by Khadija Maitaya
August 31, 2026
Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro
LABARAI

Yaki da harkar Daba a Jihar Kano

by Khadija Maitaya
August 31, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Responsabilité dans le jeu vidéo : stratégies et enjeux autour de Chicken Road 2

April 21, 2025
Yadda jajircewa tasa wani jami’in bijilanti zama kwamanda a wata karamar hukuma.

Yadda jajircewa tasa wani jami’in bijilanti zama kwamanda a wata karamar hukuma.

November 8, 2023
ADVERTISEMENT

Trending.

Masu Siye Da Siyar Da Filaye A  R/zakara Sunkoka Da Aibantasu Da Gwamnatin Kano Keyi.

Masu Siye Da Siyar Da Filaye A  R/zakara Sunkoka Da Aibantasu Da Gwamnatin Kano Keyi.

August 26, 2026
Cristiano Ronaldo Ya Auri Georgina Rodríguez

Cristiano Ronaldo Ya Auri Georgina Rodríguez

August 12, 2026
Wani Kauran Mata Ya Jikkata Wata Dattijuwa Bayan Ta Hana Shi Shiga Gurin Da Bai kamata Ba

Wani Kauran Mata Ya Jikkata Wata Dattijuwa Bayan Ta Hana Shi Shiga Gurin Da Bai kamata Ba

August 29, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Matar Aure Hukunci Bayan Samunta Da Watsa Tafasasshen Ruwa Ga Kishiyarta

Kotu Ta Yanke Wa Matar Aure Hukunci Bayan Samunta Da Watsa Tafasasshen Ruwa Ga Kishiyarta

August 7, 2026
Iran Ta Kakkabo Wasu Manyan Jiragen Yaƙi Na Amurka

Iran Ta Kakkabo Wasu Manyan Jiragen Yaƙi Na Amurka

August 14, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media