• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

NDLEA Ta Kama Mutane 6, Ta Rushe Maboyar Miyagun Kwayoyi a BUK Old Site Kano

Khadija Maitaya by Khadija Maitaya
May 4, 2026
Reading Time: 2 mins read
0
Home LABARAI
ADVERTISEMENT
466
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Hukumar hana sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Kasa (NDLEA) reshen rundunar Kano ta gudanar da wani samame a tsohuwar Jami’ar Bayero Kano (BUK Old Site), inda ta kama mutane shida da ake zargi da hannu a harkokin miyagun kwayoyi tare da rusa wasu maboyarsu.

Rahotanni sun bayyana cewa, rundunar ta dauki wannan mataki ne biyo bayan wata korafi a hukumance da mahukuntan jami’ar Bayero Kano suka gabatar mata.

RelatedPosts

Wani Matashi Ya Rasu A Gidan Budurwarsa ƴar Tik-tok Dake Unguwar Ɗanbare A Jihar Kano

Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro

Sky News: Yaƙin Trump da Iran Na Daya Daga Cikin Manyan Kurakuran Dabarun Amurka

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukumar Sadi Muhammad maigatari ya sanyawa hannu.

A karkashin shirin “Operation Sharar Mafaka”, jami’an NDLEA sun kai samame domin fatattakar mutanen da suka mayar da wasu sassan harabar jami’ar wajen safarar da kuma shan miyagun kwayoyi.

A yayin samamen, an kama mutane shida da ake zargi, tare da kwace wasu kayayyakin da ake amfani da su wajen gudanar da wadannan haramtattun ayyuka, inda aka lalata su domin hana ci gaba da amfani da su.

Da yake jawabi kan nasarar aikin, shugaban rundunar ta NDLEA a Kano , CN DY Lawal, ya ce wannan mataki na nuna kudirin hukumar wajen tabbatar da samar da muhalli mai tsabta daga miyagun kwayoyi domin dalibai, ma’aikata da iyalansu su gudanar da rayuwarsu cikin kwanciyar hankali.
“Ba za mu yi kasa a gwiwa ba. Za mu ci gaba da fatattakar dukkan maboyar miyagun kwayoyi a karkashin Operation Sharar Mafaka,” in ji shi.

Har ila yau, wannan samame ya nuna muhimmancin hadin gwiwa tsakanin NDLEA da hukumomin ilimi, inda kai rahoton da wuri da hadin kan jami’ar ya taimaka wajen daukar mataki cikin gaggawa domin kawar da barazanar da ke addabar tsaron harabar makaranta da al’umma baki daya.

Hukumar NDLEA ta Kano ta sake gargadin duk wanda ke amfani da cibiyoyin gwamnati ko na ilimi wajen safarar ko shan miyagun kwayoyi da cewa ba za a lamunci irin wadannan ayyuka ba. Har ila yau, ta bukaci al’umma da cibiyoyi da su rika kai rahoton duk wani abu da ake zargi domin gano sauran maboyar masu laifi da kuma kawar da su baki daya

Share186Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, Ya Koma Jam’iyyar National Democratic Congress (NDC) A Hukumance; Inda Ya Karɓi Katin Zama Mamba Na Jam’iyyar

Next Post

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

Khadija Maitaya

Khadija Maitaya

RelatedPosts

Wani Matashi Ya Rasu A Gidan Budurwarsa  ƴar Tik-tok  Dake Unguwar  Ɗanbare A Jihar Kano
LABARAI

Wani Matashi Ya Rasu A Gidan Budurwarsa ƴar Tik-tok Dake Unguwar Ɗanbare A Jihar Kano

by aksam
June 20, 2026
Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro
LABARAI

Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro

by Khadija Maitaya
June 19, 2026
Sky News: Yaƙin Trump da Iran Na Daya Daga Cikin Manyan Kurakuran Dabarun Amurka
LABARAI

Sky News: Yaƙin Trump da Iran Na Daya Daga Cikin Manyan Kurakuran Dabarun Amurka

by Khadija Maitaya
June 16, 2026
China Ta Soke Darussa 12,000 na Jami’o’i Domin Shirin Zamani na AI
LABARAI

China Ta Soke Darussa 12,000 na Jami’o’i Domin Shirin Zamani na AI

by Khadija Maitaya
June 14, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Kungiyar direbobi na Bus-9 sun koka da nadin sabbin shugannin NURTW na jihar kano

March 17, 2024
Rufe Gudaji Kazaure, Atiku ya zargi EFCC da take doka

Rufe Gudaji Kazaure, Atiku ya zargi EFCC da take doka

May 11, 2025
ADVERTISEMENT

Trending.

Mu Na Gayyatar  ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Ango Bulaye

Mu Na Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Ango Bulaye

June 12, 2026
An Kammala Gasar Kwallon Kafar Sada Zumunchi Dan Muna Murnar Zagayuwar Sallah Babba Cikin Nasara A Garin Nkawkawo Dake Kasar Ghana

An Kammala Gasar Kwallon Kafar Sada Zumunchi Dan Muna Murnar Zagayuwar Sallah Babba Cikin Nasara A Garin Nkawkawo Dake Kasar Ghana

June 1, 2026
The Emir of Zangon Nkawkawo, Alhaji Abdul-Nasir Usman, Extends Eid Greetings

The Emir of Zangon Nkawkawo, Alhaji Abdul-Nasir Usman, Extends Eid Greetings

June 1, 2026
Irin Yadda Ake Cigaba Da Gudanar Da  Karatun Saukar Al’qur’ani Mai Girma  A Zango Nkawkawo Dake Kasar Ghana

Irin Yadda Ake Cigaba Da Gudanar Da Karatun Saukar Al’qur’ani Mai Girma A Zango Nkawkawo Dake Kasar Ghana

June 5, 2026
Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Sha’ibu Sani Mai Atamfa (Bulaye)

Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Sha’ibu Sani Mai Atamfa (Bulaye)

June 15, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media