Daga Hassan Umar Gwammaja
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai baiwa gwamnan Kano Shawara kan harkokin yada labarai Ibrahim Adam ya fitar
Idan za a iya tunawa a makonnin da suka gabata Aksam Media ta rawaito majalisar dokokin jihar Kano ta tantance tare da Amincewa gwamnan ya nada Murtala a matsayin mataimakin gwamnan domin maye gurbin Aminu Abdussalam Gwarzo Wanda ya dauka da Kansa.
Sanarwar ta ce za a gudanar da taron rantsuwar ne a dakin taro na Coronation dake gidan gwamnatin Kano , da misalin karfe 11 na safe.
Gwamnan Kano ya karbi rahoton fitar da yan takarar APC daga ƙananan hukumomi 20, an tabbatar da wasu
Tuni dai masoya da magoya bayan Garo suke ta yin shirye-shirye domin gudanar da bukukuwa na Murnar zaman Murtala mataimakin gwamnan kano .
Masu nazari kan harkokin Siyasa suna ganin nada Murtala Sule Garo a mukamin mataimakin gwamna zai taimaka wa gwamnatin Abba musamman ta fuskar Siyasa.












