Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi wata tattaunawa ta waya da Firaministan Pakistan, Shehbaz Sharif, wacce ta ɗauki tsawon mintuna 45.
A yayin kiran, rahotanni sun nuna cewa Shugaban Iran ya yi ta maimaita godiya ga Pakistan, inda ya ke cewa: “Muna gode muku Pakistan.”
A nasa ɓangaren, Firaministan Pakistan ya riƙa taya Iran murna da abin da ya kira nasara, yana cewa: “Muna taya ku murna kan nasara.”
Haka kuma, Jagoran koli na Iran, Ali Khamenei, ya miƙa godiyarsa ga Pakistan kan goyon bayan da ƙasar ta bayar.
Rahotanni na baya-bayan nan sun nuna cewa Pakistan na taka muhimmiyar rawa wajen sasanta rikice-rikicen yankin da kuma tattaunawa tsakanin Iran da wasu ƙasashe.











