Wani kamfanin lobin siyasa da ke da hedikwata a birnin Washington, D.C., mai suna Von Batten-Montague-York, L.C., ya bayyana cewa zai matsa wa hukumomin Amurka lamba, ciki har da Shugaban ƙasar Donald Trump da ‘yan majalisar dokoki, domin kakaba takunkumi kan wasu jami’an Najeriya.
Kamfanin ya ce wannan mataki ya biyo bayan matakin da Independent National Electoral Commission (INEC) ta ɗauka na cire amincewa da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC).
A cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba, kamfanin ya nuna damuwa kan rawar da INEC ke takawa a tsarin zaɓe na Najeriya, yana mai nuni da matsalolin da aka fuskanta a baya da kuma waɗanda ke tasowa yanzu.
Sanarwar ta ƙara da cewa, “Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta Najeriya (INEC), duk da samun goyon bayan ƙasashen waje irin su Amurka da Tarayyar Turai, tana da ƙwarewa da damar gudanar da zaɓukan tarayya cikin gaskiya da sahihanci.”












