Sojojin Iran sun ce sun kai hare-hare da jirage marasa matuka kan wuraren ajiyar jiragen yaki, da cibiyoyin sadarwa na tauraron dan Adam da kuma wuraren ajiyar makamai da ke sansanin sojin saman Amurka na Ahmad al-Jaber a Kuwait.
Hare-haren da Iran ta ce kai na zuwa a daidai lokacin da Pakistan da ke shiga tsakani a rikicin Washington da Teheran ta ce ana ci gaba da tattaunawa a tsakanin bangarorin biyu.










