Rahotanni na nuni da cewa akalla mutane takwas ake fargabar suka mutu bayan da wani ginin bene mai hawa daya ya rufta a unguwar Kuntau da ke karamar hukumar Kumbotso a jihar Kano.
Lamarin ya faru ne da sanyin safiyar Ranar Juma’a a yayin da ma’aikata ke aikin gini a wannan Gida.
Majiyoyi masu tushe daga yankin sun bayyana cewa akalla mutane 15 ne ciki har da mai ginin suka makale a lokacin da ibtila”in ya faru.
Maigidan, wanda ake kira Sharu, yana gina sabon bene don haɗa shi da gidan da yake ciki.
Rahotanni sun ce wasu daga cikin mutanen da suka makale a cikin gini sun zo wuce wa ne suka nemi mafaka saboda ruwan sama.
Rahoton ya ce an garzaya da mutane bakwai asibitin kwararru na Murtala Muhammad, kuma mutum daya ya mutu a kan hanyar su ta zuwa asibitin.
Zuwa lokacin hada wannan rahoto mun tuntubi jami’in hulda da jamaa na Hukumar Kashe gobara ta whatapp Amma bai Sami yi mana cikakken bayani ba.












