Daga Sani Abdurrazak Darm
Biyo bayan samun korafe-korafe na yiwa Mata sata a Jakunkunan su da kuma kasa kaya akan hanya a Kasuwar Rimi Danja, zuwa jikin Asibitin Murtala, da hakan yake haifar da cinkoson Ababen hawa.
Yanzu haka hukumar Karota karkashin jagorancin OC Cigari, ta jagoranci tashin mutanen da suke kasa kaya a kan titin, domin gudanar da aikin, batare da bata lokaci ba.
Sanin kowa ne wannan waje ya zama wani sansani na cunkoso, baya ga zargin kwace n waya, da satar kayan mutane, Wanda hakan yasanya hukumar karota ta himmatu wajen kawar da duka masu kasa kayan, tare da samun damar kai Marasa Lafiya cikin Asibiti a saukake.
Wakilin Aksammedia Abubakar S Gwammaja ya Ziyarci Danjan Asibitin Murtala domin ganin yadda aikin ya gudana bisa jagorancin Abdukarim Cigari.. ku ya zanta da wasu mutane, ko yaya suka kalli gyaran, kuma Kwalliya zata biya kudin Sabulu.
Cue in…..insert
Muhammad Abdullahi Shine Shugaban ‘yan Kasuwa na bakin Danjar Asibitin Murtala, ya sheda cewa wannan gyara yayi kyau, dama sun jima suna gira ga Gwamnati a kawo dauki, a tashi mutanen da suke kasa kaya akan titin domin a samu damar kai Mutanen da suka kamu da rashin lafiya, ko hadarin.
Abubakar Muhammad Sharada shine Kakakin Hukumar Karota, ya bayyana cewa sakamakon cinkoso, da rufe hanyar hukumar ta bawa OC Cigari damar gyara wajen, kuma duk inda ake kasa kaya hukumar Karota zata hana.
Hausawa dai sun CE gyara kayan ka, baya hana sauke muraba….bin doka akace wayewa.












