• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Mutane 25 sun mutu 800 sun jikkata a wata gagarumar fashewa

aksam by aksam
April 27, 2025
Reading Time: 2 mins read
0
Home LABARAI
ADVERTISEMENT
468
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

RelatedPosts

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Ya Sanya Ranar Talata 05 GA watan Mayu 2026, A Matsayin Ranar Da Zai Jagoranci Rantsar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

NDLEA Ta Kama Mutane 6, Ta Rushe Maboyar Miyagun Kwayoyi a BUK Old Site Kano

Hukumomi a Iran, sun ce aƙalla mutum 25 ne suka mutu, wasu 800 kuma suka jikkata a wata gagarumar fashewa da ta auku a Daya daga cikin manyan tasoshin jirgen ruwan ƙasar.

Har yanzu ba a tabbatar da abin da ya haddasa fashewar ba a tashar Shahid Rajaee, inda har yanzu wutar ke ci, amma kuma kafofin yada labarai na kasar na nuna yuwuwar hannun Isra’ila a lamarin.

Fashewar wadda ta auku ranar Asabar da safe ta kasance ne a daya daga cikin manyan tashoshin jirgin ruwa na kasuwanci, da ke kusa da birnin Bandar Abbas na kudanci.

Fashewar ta lalata motoci da tagogi da rufin gine-ginen da ke kusa da wajen . Sannan mazauna unguwannin da ke nisan kilomita 30 sun ji kararta.

BBC ta tabbatar da sahihancin wasu hotunan bidiyo da ke nuna wuta na ci ganga-ganga kafin fashewar da da ta auku a wani gidan ajiyar kaya, inda mutane ke gudun tsira da kuma wasu yashe cikin jini a gefen titi kusa da tarkacen da ke cin wuta.

Hoton da aka dauka daga sama ya nuna akalla wuri uku da wutar ke ci inda ministan harkokin cikin gida ya tabbatar da cewa wutar na bazuwa daga sunduki ko kwantaina zuwa kwantaina .

An bayar da umarnin da kada a bude makarantun da ke kusa da wajen a ranar Lahadi.

Wani kamfanin al’amuran da suka shafi tsaro na ruwa ya ce yana ganin kwantainonin da wutar ta tashi suna dauke ne da makamashin da za a hada makamai masu linzami ne da su.

Kamfanin na Ambrey Intelligence ya ce yana ganin wutar ta tashi ne sakamakon rashin alkinta makamashin yadda ya dace.

Kamfanin ya kara da cewa yana sane cewa wani jirgin ruwa na Iran ya sauke wannan makamashi a tashar ruwan a watan Maris da ya gabata.

Ko a can baya daman jaridar Financial Times ta ruwaito cewa wasu jiragen ruwa biyu sun yi dakon makamashi daga China zuwa Iran.

Share187Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Wata Kotu A Jihar Kano Ta Yanke Wa Wani Mutum Hukuncin Daurin Watanni Biyu Bisa Sare Bishiyu Ba Akan Ka’ida Ba

Next Post

Kaddara Ce Ta Hadani Da Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, Amma Dabi’ata Batazo Daya Da Tasa Ba:- Dakta Beffa Bichi

aksam

aksam

RelatedPosts

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Ya Sanya Ranar Talata 05 GA watan Mayu 2026, A Matsayin Ranar Da Zai Jagoranci Rantsar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan
LABARAI

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Ya Sanya Ranar Talata 05 GA watan Mayu 2026, A Matsayin Ranar Da Zai Jagoranci Rantsar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan

by aksam
May 4, 2026
Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano
LABARAI

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

by aksam
May 4, 2026
NDLEA Ta Kama Mutane 6, Ta Rushe Maboyar Miyagun Kwayoyi a BUK Old Site Kano
LABARAI

NDLEA Ta Kama Mutane 6, Ta Rushe Maboyar Miyagun Kwayoyi a BUK Old Site Kano

by Khadija Maitaya
May 4, 2026
Tsohon Dan Takarar Shugaban Kasa A  Jam’iyyar Labour Party, Peter Obi, Ya Sanar Da Ficewarsa Daga  Jam’iyyar Haɗaka Ya ADC
LABARAI

Tsohon Dan Takarar Shugaban Kasa A Jam’iyyar Labour Party, Peter Obi, Ya Sanar Da Ficewarsa Daga Jam’iyyar Haɗaka Ya ADC

by aksam
May 3, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Yanzu-yanzu CBN ya sauke farashin Dalar Amurka warwas

Yanzu-yanzu CBN ya sauke farashin Dalar Amurka warwas

April 23, 2024
Gwamna Kano Abba Kabir Yusuf:-  Ya Rantsar Da Sabon Kwamashin Tsaron Cikin Gida

Gwamna Kano Abba Kabir Yusuf:- Ya Rantsar Da Sabon Kwamashin Tsaron Cikin Gida

August 16, 2024
ADVERTISEMENT

Trending.

Mu Na Gayyatar  ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Comr.  Usaini Sani Adamu !!!

Mu Na Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Comr. Usaini Sani Adamu !!!

April 24, 2026
Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Umar SA’ID

Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Umar SA’ID

April 20, 2026
Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

May 4, 2026
Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID

Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID

April 17, 2026
Atiku, Kwankwaso , Obi Sun Jagoranci Zanga-Zanga A Babban Birnin Tarayya Abuja

Atiku, Kwankwaso , Obi Sun Jagoranci Zanga-Zanga A Babban Birnin Tarayya Abuja

April 8, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media