FCT Abuja – Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu na ganawar sirri yanzu haka da manyan hafsoshin tsaron ƙasar nan a Ado Villa da ke birnin tarayya Abuja.
Taron dai na gudana ne karkashin majalisar tsaro ta Najeriya a fadar shugaban ƙasa yau Litinin, 5 ga watan Agusta, 2024 yayin da ake tsaka da zanga-zanga.
Babban hafsan tsaro na ƙasa, Janar Christopher Musa ne ya jagoranci hafsoshin tsaro da sauran shugabannin hukumomin tsaro zuwa taron, kamar yadda Vanguard ta rahoto.
Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da matasa ke ci gaba da gudanar da zanga-zangar adawa manufofin gwamnatin Tinubu da suka kawo da yunwa a kasar.
Karin bayani na nan tafe.










