A yau, Juma’a ne wata babbar kotun tarayya za ta saurari ƙarar da Sarkin Kano na 15 Aminu Ado Bayero ya shigar gabanta, inda yake neman kotun ta hana kama shi, sannan kuma a mayar da shi gidan sarki na ƙofar kudu.
Cikin waɗanda sarkin ya shigar da su ƙarar har da ƴansanda da jami’an tsaro na civil defence.
Ranar 28 ga watan Mayu mai shari’a Amobeda Simon ya bayar da umarnin cewa waɗanda ake ƙarar kada wanda ya hana shi shiga gidan sarki na kofar kudu ko hana shi amfani da duk wasu abubuwan da ya cancanta a matsayin sarki.
Sannan umarnin kotun ya ce kada fitar da duk wanda yake cikin gidan sarki ba bisa ka’ida ba, har zuwa lokacin da kotun za ta saurari buƙatar da aka gabatar mata.












