Yan majalisar wakilan Najeriya da suka fito daga arewa maso yammacin ƙasar, sun bukaci gwamnatin tarayya da hukumomin tsaron kasar su sauya salon yadda suke tunkarar matsalar tsaro a yankin.
‘Yan majalisar sun ce duk da cewar bangarorin da ke yaki da matsalar tsaron na aiki tare, amma akwai bukatar samun fahimtar juna musamman a bangaren gwamnoni da tarayya don ganin an ci nasara a yaki da ‘yan bindigar da suka addabi yankin.
Hon. Aminu Sani Jaji, na daga cikin ‘yan majalisar yankin da suka gudanar da taro a kan wannan bukata a Abuja babban birnin tarayar kasar, kuma a tattaunawarsa da BBC ya ce, yankin arewa maso yamma shi ne ya fi yawan al’umma da kuma fuskantar matsalar tsaro a yanzu gashi kuma anan ne aka fi noma.
Ya ce,”Babban abin da ya damemu shi ne yadda matsalar tsaro ta rage yadda ake noma a wannan yanki namu, abin da ake nomawa ada kafin matsalar tsaro a yanzu ko kwatansa ba a nomawa saboda akwai wurare da dama da ba a nomanma kwata-kwata.”









