Wasu da ake zargin ’yan bindiga ne sun kai farmaki a kauyen Karaɗuwa da ke ƙaramar hukumar Matazu a Jihar Katsina, inda suka sace wani basarake mai daraja a yankin
Wannan farmaki ya faru ne da safiyar ranar Juma’a, 5 ga watan Yuli, 2025 da misalin ƙarfe 3:30 na asuba, yayin da maharan suka isa kauyen dauke da muggan makamai a kan babura, inda suka kutsa kai cikin gidan Wakilin Hakimin Matazu a kauyen Karaɗuwa, Alhaji Abdullahi Muhammadu Bello, suka kuma yi awon gaba da shi.
’Yan Sanda Sun Kama Matasa 5 Da Ake Zargi Da Kwacen Waya A Adaidaita Sahu
Rahoton da muka samu ya tabbatar da cewa maharan sun harba bindiga a sama don tsoratar da mazauna yankin kafin su fice da basaraken zuwa daji.
Wani mai bibiyar lamurran tsaro a shafin X, wanda aka fi sani da Bakatsine, ya tabbatar da faruwar harin inda ya ce:
“A daren jiya, ’yan bindiga sun sace Magajin Garin Karaɗuwa, Alhaji Abdullahi Bello. Karaɗuwa na ƙarƙashin ƙaramar hukumar Matazu ce a Jihar Katsina.”
Zuƙekiyar daukar matakin gaggawa daga jami’an tsaro bai kai ga ceto basaraken ba, sai dai rundunar ’yan sanda ta ce tana ci gaba da gudanar da bincike tare da sintiri domin gano inda aka boye shi da kuma kamo masu laifi.
Rundunar ’Yan Sanda Ta Tarwatsa ’Yan Bindiga a Dutsinma, Ta Ceto Fursunoni
A wani harin daban da ya faru a cikin dare na ranar Juma’a, ’yan sanda a Jihar Katsina sun samu nasarar dakile wani hari da ’yan bindiga suka kai a ƙaramar hukumar Dutsinma.
Harin ya faru ne da misalin ƙarfe 9:45 na dare a unguwar Bayan Masallaci, kusa da Sabon Garin Safana, inda maharan suka yi garkuwa da wasu mazauna yankin.
Bayan samun kiran gaggawa daga mutanen yankin, DPO na Dutsinma ya hanzarta tura jami’ansa tare da motar yaki ta APC, inda suka ci karo da maharan a wajen garin Gidan Maifanfo, kuma aka yi musayar wuta mai zafi da su.
A cewar rahotanni, an samu nasarar ceto mutane biyu — Aminu Sani da Zainab Sani — daga hannun maharan, yayin da wani mutum mai suna Musa Sani ya samu harbin bindiga a kugunsa, wanda aka garzaya da shi zuwa Asibitin Gwamnati na Dutsinma domin samun kulawa.
Wata majiya daga rundunar ’yan sanda ta tabbatar da cewa ana ci gaba da ƙoƙarin ceto basaraken da aka sace a Karaɗuwa, tare da ɗaukar matakai na kara sa ido a kananan hukumomi da ke da rauni wajen fuskantar hare-hare.
Haka kuma, jami’an tsaro sun shawarci jama’a da su ci gaba da bayar da hadin kai da kuma gaggauta kai rahoto idan sun ga wani motsi da ba su amince da shi ba.











