Bashir Ahmad ya yi magana kan yiwuwar sauya sheƙar ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NNPP a zaɓen 2023, Rabi’u Kwankwaso, zuwa APC
Wannan dai na zuwa ne bayan da ɗaya daga cikin jiga-jigan jam’iyyar APC, Bisi Akande, ya haɗu da Kwankwaso a kwanan nan
Tsohon hadimin na Buhari, Bashir Ahmad ya nuna cewa ana maraba da Kwankwaso da mabiyansa a jam’iyyar APC
Kwankwaso wanda ya kasance mai riƙe da tutar jam’iyyar NNPP a zaɓen shugaban ƙasa na 2023, ya zama abin magana a ƙarshen makon nan, bayan an ganshi tare da Bisi Akande, wani gogaggen ɗan siyasa kuma jigo a jam’iyyar APC.
Wannan dai na zuwa ne sa’o’i kaɗan bayan da wani ɓangare na jam’iyyar NNPP ya tabbatar da cewa korar Kwankwaso na nan daram, kuma akwai wani sabon raɗe-raɗin cewa zai sauya sheka
Da yake mayar da martani kan lamarin a wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X a ranar Lahadi, 21 ga watan Janairu, Bashir Ahmad ya bayyana cewa APC za ta yi murnar karɓar Kwankwaso zuwa cikin jam’iyyar.












