Gwamnatin jihar kano ta ce masu zanga-zangar sun sace Muhimman takardun da ake ake tuhumar tsohon gwamnan jihar Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa da Kuma wasu daga cikin mukarraban gwamnatinsa .
Gwamna jihar kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ne ya bayyana hakan yayin da ya ziyarci harabar babbar kotun jihar dake sakatariyar Audu Bako.
A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Kano Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar tace gwamnan ya nuna damuwa kan abun da ya faru na lalata dukiyoyi masu tarin yawa a kotun, tare da sace muhimman takardun tuhumar da ake yiwa shugaban jam’iyyar APC na kasa Dr. Abdullahi Umar Ganduje.










