Daga Hassan Umar Gwammaja
Gwamnan jihar Jigawa Malam Umar Namadi ya rasa ɗansa mai suna Abdulwahab Umar Namadi, wanda ya bar duniya da yammacin yau Alhamis sakamakon wani mummunan hatsarin mota da ya afku a kan titin Dutse zuwa Kafin-Hausa.
Ana kuma gudanar da jana’izarsa a garin Kafin Hausa kamar yadda addinin Musulunci ya tanadar.
Marigayin mai shekaru 24, shi ne babban ɗan gwamnan inda ya rasu ya bar iyayensa da ƙannensa maza da mata .
Hajiya Maryam Namadi mahaifiya ce ga Gwamnan na Jigawa wadda ita ma ta rasu a jiya Laraba, bayan ta yi fama da gajerar rashin lafiya a asibitin koyarwa na Malam Aminu Kano (AKTH) kuma an yi jana’izarta a jiyan.
An kuma binne ta ne da misalin ƙarfe 4:30 na yamma a garinsu kamar yadda addinin musulunci ya tanada.
Gwamna Namadi dai ya tafi kasar Sin ne domin ziyarar aiki, inda bayan samun labarin rasuwar mahaifiyar tasa ne ya dawo da safiyar yau Alhamis.











