• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Gwamnatin Kano ta yi bayani Akan cecekucen da ake yi Akan dokar lefe

aksam by aksam
January 19, 2024
Reading Time: 2 mins read
0
Home LABARAI
ADVERTISEMENT
475
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Gwamnatin jihar Kano ta yi bayani ƙarara kan tanade-tanaden dokar aure da take ta janyo muhawara a jihar da sauran shafukan sada zumunta.

Gwamnatin Kano ta bakin kwamishinan shari’a na jihar Barista Haruna Isa Dederi ta ce tabbas akwai dokar da ta yi bayani dalla-dalla kan yadda ya kamata mutane su riƙa gudanar da auratayyarsu a jihar.

RelatedPosts

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Ya Sanya Ranar Talata 05 GA watan Mayu 2026, A Matsayin Ranar Da Zai Jagoranci Rantsar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

NDLEA Ta Kama Mutane 6, Ta Rushe Maboyar Miyagun Kwayoyi a BUK Old Site Kano

tattaunawarsa da BBC Haruna Dederi ya ce dokar ta yi bayani kan mene ne ya halasta da kuma mene ne aka haramta idan an tashi aure a jihar Kano.

“Ba iya lefe kawai dokar ta haramta ba, amma a yanzu shi ne abin da ya fi ɗaukar hankalin al’umma,” in ji kwamishinan.

“Lokaci zuwa lokaci akan sake bibiyar doka, domin sake mata fasali idan muƙatar hakan ta taso.

“Tsayin zamani da kuma buƙatuwar mutane kan sa a sauya doka, ko kuma a yi mata kwaskwarima. Kamar dai yadda ake yi wa kundin tsarin mulki na ƙasa,” in ji Barr. Dederi.

Ya ce a iya saninsa babu wanda ya gabatar da bibiyar wannan doka domin sabunta ta, ko kuma sauya mata fasali.

A cewarsa matuƙar akwai doka, duk tsayin zamani idan ba a yi mata gyara ba tana nan a matsayin doka babu mai sauya hukuncinta.

An tambayi Dederi kan me yasa dokar ta ɗauki kusan shekara 36 amma da dama cikin al’umma ba su santa ba?

Ya ce ƙalubale ne masu yawa da suke janyo haka, inda ya fara da zayyana yawan dokokin da ake da su a tarayya da jihohi. ya kuma ba da shawarar kamata ya yi a haɗa kundin wuri guda domin taƙaita yawan dokokin.

Ƙalubale na biyu shi ne ɓangaren shari’a na buƙatar a riƙa wayar da kai kan irin waɗannan dokoki. Saboda ƙuduri baya zama doka sai ya bi matakai da dama, tun a lokacin matakan ya kamata a riƙa sanar da al’uma a kanta.

Kazalika idan majalisar dokoki ta jiha ta tabbatar da doka ya kamata a riƙa samar da sashe da zai riƙa shaidawa mutane dokar.

Masu aiwatar da dokar ma ya kamata su riƙa ilimantar da mutane game da dokokin da ake yi musu hukunci a kai, ba zai ranar da hukunci ya zo ba mutum ya ji ta a matsayin sabuwar doka a kansa.

Kwamishinna Haruna Isa Dederi ya amsa cewa akwai ƙarancin wayar da kan al’umma game da dokokin rayuwa da suka shafe su, wanda kuma haka aikin gwamnati ne.

Share190Tweet119SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

An Gudanar da taron karkarshe shirin Care’s lafiyan yara da Kamfanin hada magunguna na PFIZER da cibiyar kula da lafiya t CARE suka shirya.

Next Post

aksam

aksam

RelatedPosts

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Ya Sanya Ranar Talata 05 GA watan Mayu 2026, A Matsayin Ranar Da Zai Jagoranci Rantsar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan
LABARAI

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Ya Sanya Ranar Talata 05 GA watan Mayu 2026, A Matsayin Ranar Da Zai Jagoranci Rantsar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan

by aksam
May 4, 2026
Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano
LABARAI

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

by aksam
May 4, 2026
NDLEA Ta Kama Mutane 6, Ta Rushe Maboyar Miyagun Kwayoyi a BUK Old Site Kano
LABARAI

NDLEA Ta Kama Mutane 6, Ta Rushe Maboyar Miyagun Kwayoyi a BUK Old Site Kano

by Khadija Maitaya
May 4, 2026
Tsohon Dan Takarar Shugaban Kasa A  Jam’iyyar Labour Party, Peter Obi, Ya Sanar Da Ficewarsa Daga  Jam’iyyar Haɗaka Ya ADC
LABARAI

Tsohon Dan Takarar Shugaban Kasa A Jam’iyyar Labour Party, Peter Obi, Ya Sanar Da Ficewarsa Daga Jam’iyyar Haɗaka Ya ADC

by aksam
May 3, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

INEC Ta Saka Ranakun Zaɓen 2027

INEC Ta Sanya Ranar Zaben Cike Gurbi Na Kujerar ‘Yan majalisar Tarayya A Kano Da Sasu Jihohi

May 1, 2026
Bayan shigar Najeriya kungiyar Samoa, wata jiha ta fara fuskantar barazanar masu muradan auren jinsi

Yadda masana da manyan yansiyasa suka caccaki shugaba Tinubu

August 5, 2024
ADVERTISEMENT

Trending.

Mu Na Gayyatar  ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Comr.  Usaini Sani Adamu !!!

Mu Na Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Comr. Usaini Sani Adamu !!!

April 24, 2026
Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Umar SA’ID

Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Umar SA’ID

April 20, 2026
Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

May 4, 2026
Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID

Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID

April 17, 2026
Atiku, Kwankwaso , Obi Sun Jagoranci Zanga-Zanga A Babban Birnin Tarayya Abuja

Atiku, Kwankwaso , Obi Sun Jagoranci Zanga-Zanga A Babban Birnin Tarayya Abuja

April 8, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media