• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Gwamnatin Kano ta yi bayani Akan cecekucen da ake yi Akan dokar lefe

aksam by aksam
January 19, 2024
Reading Time: 2 mins read
0
Home LABARAI
ADVERTISEMENT
475
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Gwamnatin jihar Kano ta yi bayani ƙarara kan tanade-tanaden dokar aure da take ta janyo muhawara a jihar da sauran shafukan sada zumunta.

Gwamnatin Kano ta bakin kwamishinan shari’a na jihar Barista Haruna Isa Dederi ta ce tabbas akwai dokar da ta yi bayani dalla-dalla kan yadda ya kamata mutane su riƙa gudanar da auratayyarsu a jihar.

RelatedPosts

Wani Matashi Ya Rasu A Gidan Budurwarsa ƴar Tik-tok Dake Unguwar Ɗanbare A Jihar Kano

Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro

Sky News: Yaƙin Trump da Iran Na Daya Daga Cikin Manyan Kurakuran Dabarun Amurka

tattaunawarsa da BBC Haruna Dederi ya ce dokar ta yi bayani kan mene ne ya halasta da kuma mene ne aka haramta idan an tashi aure a jihar Kano.

“Ba iya lefe kawai dokar ta haramta ba, amma a yanzu shi ne abin da ya fi ɗaukar hankalin al’umma,” in ji kwamishinan.

“Lokaci zuwa lokaci akan sake bibiyar doka, domin sake mata fasali idan muƙatar hakan ta taso.

“Tsayin zamani da kuma buƙatuwar mutane kan sa a sauya doka, ko kuma a yi mata kwaskwarima. Kamar dai yadda ake yi wa kundin tsarin mulki na ƙasa,” in ji Barr. Dederi.

Ya ce a iya saninsa babu wanda ya gabatar da bibiyar wannan doka domin sabunta ta, ko kuma sauya mata fasali.

A cewarsa matuƙar akwai doka, duk tsayin zamani idan ba a yi mata gyara ba tana nan a matsayin doka babu mai sauya hukuncinta.

An tambayi Dederi kan me yasa dokar ta ɗauki kusan shekara 36 amma da dama cikin al’umma ba su santa ba?

Ya ce ƙalubale ne masu yawa da suke janyo haka, inda ya fara da zayyana yawan dokokin da ake da su a tarayya da jihohi. ya kuma ba da shawarar kamata ya yi a haɗa kundin wuri guda domin taƙaita yawan dokokin.

Ƙalubale na biyu shi ne ɓangaren shari’a na buƙatar a riƙa wayar da kai kan irin waɗannan dokoki. Saboda ƙuduri baya zama doka sai ya bi matakai da dama, tun a lokacin matakan ya kamata a riƙa sanar da al’uma a kanta.

Kazalika idan majalisar dokoki ta jiha ta tabbatar da doka ya kamata a riƙa samar da sashe da zai riƙa shaidawa mutane dokar.

Masu aiwatar da dokar ma ya kamata su riƙa ilimantar da mutane game da dokokin da ake yi musu hukunci a kai, ba zai ranar da hukunci ya zo ba mutum ya ji ta a matsayin sabuwar doka a kansa.

Kwamishinna Haruna Isa Dederi ya amsa cewa akwai ƙarancin wayar da kan al’umma game da dokokin rayuwa da suka shafe su, wanda kuma haka aikin gwamnati ne.

Share190Tweet119SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

An Gudanar da taron karkarshe shirin Care’s lafiyan yara da Kamfanin hada magunguna na PFIZER da cibiyar kula da lafiya t CARE suka shirya.

Next Post

aksam

aksam

RelatedPosts

Wani Matashi Ya Rasu A Gidan Budurwarsa  ƴar Tik-tok  Dake Unguwar  Ɗanbare A Jihar Kano
LABARAI

Wani Matashi Ya Rasu A Gidan Budurwarsa ƴar Tik-tok Dake Unguwar Ɗanbare A Jihar Kano

by aksam
June 20, 2026
Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro
LABARAI

Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro

by Khadija Maitaya
June 19, 2026
Sky News: Yaƙin Trump da Iran Na Daya Daga Cikin Manyan Kurakuran Dabarun Amurka
LABARAI

Sky News: Yaƙin Trump da Iran Na Daya Daga Cikin Manyan Kurakuran Dabarun Amurka

by Khadija Maitaya
June 16, 2026
China Ta Soke Darussa 12,000 na Jami’o’i Domin Shirin Zamani na AI
LABARAI

China Ta Soke Darussa 12,000 na Jami’o’i Domin Shirin Zamani na AI

by Khadija Maitaya
June 14, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Revolutionizing Gaming Experiences: The Role of Pirots in Modern Esports

April 21, 2025

Bezpieczeństwo i regulacje w branży hazardowej online

April 21, 2025
ADVERTISEMENT

Trending.

Mu Na Gayyatar  ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Ango Bulaye

Mu Na Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Ango Bulaye

June 12, 2026
An Kammala Gasar Kwallon Kafar Sada Zumunchi Dan Muna Murnar Zagayuwar Sallah Babba Cikin Nasara A Garin Nkawkawo Dake Kasar Ghana

An Kammala Gasar Kwallon Kafar Sada Zumunchi Dan Muna Murnar Zagayuwar Sallah Babba Cikin Nasara A Garin Nkawkawo Dake Kasar Ghana

June 1, 2026
The Emir of Zangon Nkawkawo, Alhaji Abdul-Nasir Usman, Extends Eid Greetings

The Emir of Zangon Nkawkawo, Alhaji Abdul-Nasir Usman, Extends Eid Greetings

June 1, 2026
Irin Yadda Ake Cigaba Da Gudanar Da  Karatun Saukar Al’qur’ani Mai Girma  A Zango Nkawkawo Dake Kasar Ghana

Irin Yadda Ake Cigaba Da Gudanar Da Karatun Saukar Al’qur’ani Mai Girma A Zango Nkawkawo Dake Kasar Ghana

June 5, 2026
Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Sha’ibu Sani Mai Atamfa (Bulaye)

Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Sha’ibu Sani Mai Atamfa (Bulaye)

June 15, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media