Kasuwanci da sauran ayyukan yau da kullum sun Sami tsaiko a jihar Legas tun jiya laraba biyo bayan shafe sa’o’i 10 Ana ruwan Sama Lamar da bakin kwarya.
A cewar gwamnatin jihar Legas ruwan an fara shi ne tun tsakiyar dare har yamma inda ya shafe awo tara zuwa 12 Yana zuba.
Kazalika an Sami ambaliya mai karfi a wasu unguwanni ciki har da yankin Mushin inda gini mai hawa biyu ya rushe kuma ya tare hanya kana ya haifar da tsaiko ga mazauna unguwar ciki har da Yara Yan makaranta.
Ambaliyar ta shafi unguwanni irin su Berger, Ikeja, Ogba, Iyana-Oworo, Agege, Ijegun-Isheri Osun, Gbagada da kuma Lagos Island.
A nasa jawabin sakataren Hukumar bada agajin gaggawa Olufemi Oke-Osanyintolu, na jihar Legas Yace sun ceto mutane bakwai a raye cikin ginin da ya rushe.












