Hukumar yaƙi da masu yiwa tattalin arziƙin ƙasa zagon ƙasa (EFCC), ta sanar da jama’a maƙarƙashiyar da ake ƙulla mata.
Hukumar EFCC ta bayyana cewa akwai wani shiri da wasu ƙungiyoyi ke yi domin tayar da zanga-zangar nuna adawa da hukumar.
Hukumar ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawunta, Dele Oyewale, ya sanya a shafin X na hukumar.
EFCC ta ce a cikin ƴan kwanakin da suka gabata, ƙungiyoyin sun yi kamfen sosai a shafukan sada zumunta, inda suka ɗauki haziƙan matasan Najeriya, ciki har da ɗalibai domin nuna adawa da ayyukanta.
Ta ce ana ci gaba da gudanar da wannan kamfen ɗin ne domin nuna turjiya kan ayyukan hukumar musamman ta fuskar aiwatar da dokokin da suka shafi aikata laifukan yanar gizo.
Jawabin da hukumar EFCC ta fitar
“Hukumar, duk da cewa ba ta nuna adawa da zanga-zangar da ƴan ƙasa ke da ikon yi ba, ta damu bisa shaidun da ke nuna wani shiri na wasu gurɓatattu da hukumar ke bincika ko tuhuma domin yin amfani da zanga-zangar su tayar da hargitsi a ƙasa.”
“A matsayin hukumar tabbatar da doka da oda, hukumar ba za ta amince da duk wani shirin yiwa doka karan tsaye ba a ko’ina a cikin ƙasar nan musamman a kusa da ofisoshinta a faɗin Najeriya.”
“EFCC, tare da sauran hukumomin tsaro na aiki domin ɗaukar matakan da suka dace wajen magance matsalolin da ke barazana ga zaman lafiya da tsaron Najeriya.”












