Daga Hassan Umar Gwammaja
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da haka fitar a yau mai dauke da sa hannun mai taimakawa shugaban kasa akan harkokin yalda labarai, Ajuri Ngalale.
Nada Farfesa Abdullahi Saleh Usman ya biyo bayan dakatar da tsohon shugaban hukumar Jalal Arabi wanda ake zarginsa da almundahanar kudaden tallafin hajjin shekara ta 2024.
Nadin Farfesa Abdullahi Saleh Usman zai tabbata ne idan Majalisar dattawa sun amince da nadin.












