Daga Hassan Umar Gwammaja
Gwamnan jihar Alhaji Abba Kabir Yusuf ne ya jagoranci bayar da diyar yau a ɗakin taro na Afrika House da ke fadar gwamnatin jihar, Yusuf ya tabbatar da cewa dukkannin wasu gonaki da gwamnatin ta karɓa domin mayar da su alƙarya, gwamnatin sa za ta tabbatar da biyan dukkannin ma-mallaka guraren haƙƙoƙin su.
Gwamnan ya ƙara da cewa ganin yadda al’umma suke ƙaruwa a faɗin jihar Kano, ya zama wajibi gwamnati ta ƙara samar da guraren da al’umma zasu zauna domin gudanar da rayuwar su cikin nutsuwa da kwanciyar hankali.
A cewar sa, “Yayin karɓar gonakin anyi duba da yanki da suke da ƙaracin ci gaba, hakan yasa gwamnati ta zaɓi yankunan nasu, domin zamanantar da su wajen zama cikakkiyar alƙarya kamar yadda cikin birni take dashi, “in ji Abba Kabir”.
Malan Sani Abba guda ne daga cikin jagororin rijiyar gwangwan, ya bayyana farin cikin su kan yadda suka karɓi wannan diyar.











