An ƙara mafi ƙarancin albashi A wani labarin kuma, kun ji cewa gwamnan jihar Edo, Godwin Obaseki, ya bayyana N70,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi ga ma’aikatan.
Gwamna Obaseki ya sanar da haka ne yayin ƙaddamar da sabon ofishin ƴan kwadago na jihar, inda ya ce sabon mafi ƙarancin albashin zai fara aiki ne daga ranar, 1 ga watan Mayun 2024.
Itama a nata bangaren Gwamnatin tarayya ƙarƙashin jagorancin shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ta sanar da yi wa ma’aikata ƙarin albashi
Ma’aikatan da ke kan tsarin albashi na bai ɗaya za su samu ƙarin albashi da kaso 25% zuwa kaso 30% a kan wanda suke karɓa a yanzu
Sakataren yaɗa labarai na hukumar kula da albashi ta ƙasa ya sanar da hakan inda ya ƙara da cewa ƙarin albashin zai fara aiki ne daga ranar, 1 ga watan Janairun 2024











