• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Shugaba Bola Tinubu, Ya Amince Wa Kamfanin Man Fetur Na Ƙasa (NNPCL), Da Ya Yi Amfani Da Ribar Shekarar 2023 Da Aka Mamu Domin Biyan Tallafin Man Fetur.

aksam by aksam
August 19, 2024
Reading Time: 1 min read
0
Home SIYASA
ADVERTISEMENT
468
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Daga Hassan Umar Gwammaja

Wata majiya ta rawaito shugaban ya kuma amince da dakatar da biyan riba da aka samu a 2024 ga gwamnati don taimakawa da kuɗaɗen da kamfanin zai kashe.

RelatedPosts

Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, Ya Koma Jam’iyyar National Democratic Congress (NDC) A Hukumance; Inda Ya Karɓi Katin Zama Mamba Na Jam’iyyar

Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Mohammed Ya Fice Daga Jam’iyar PDP

Wasu Dalilin Da Suka Sa Kwankwaso Ke Shirin Ficewa Daga Jam’iyyar ADC

Ko da yake Tinubu ya sanar da cire tallafin man fetur a ranar 29 ga watan Mayu, 2023, sai dai akwai alamun da ke nuna cewar har yanzu gwamnati na kashe kuɗaɗe masu yawa a kan tallafin.

Idan ba a manta ba, ‘yan Najeriya sun yi zanga-zanga saboda wahalar da ake ciki a ƙasar, kuma ɗaya daga cikin buƙatunsu shi ne a dawo da tallafin man fetur.

Amma a cikin wani jawabin da Tinubu ya yi, ya bayyana cewa dawo da tallafin man fetur ba zai yiwu ba, inda ya bayyana cire tallafin a matsayin abu mai wahala amma kuma wajibi ne gwamnatinsa ta yi.

Ya ce tallafin ya kasance tamkar wata sarƙa da ta ɗaure tattalin arziƙin Najeriya.

A ranar Litinin, wata jarida a Intanet ta ruwaito cewa Tinubu ya amince wa NNPCL da ya biya tallafin bayan da kamfanin ya koka cewa ya yi amfani da duk hanyoyin da zai iya don samar da isasshen man fetur a ƙasar nan amma hakan ya gagara.

NNPCL ya shaida wa shugaban cewa waɗannan ƙoƙarin sun gaza warware matsalar da ake fuskanta, kuma idan ba a biya tallafin ba, kamfanin ba zai iya sanya kuɗin da ake buƙata daga gare shi ga asusun Gwamnatin Tarayya ba.

Don haka, Tinubu ya umarci kamfanin da ya yi amfani da haraji da sauran kuɗaɗen da aka ware wa Gwamnatin Tarayya domin biyan kuɗaɗen tallafin man fetur.

Share187Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Jam’iyyar APC Reshen Jihar Kano, Ta Bukaci Hukumar EFCC Gudanar Da Cikakken Bincike A Kan Badakalar Zargin Kwangilar Samar Da Magunguna

Next Post

Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu Ya Amince Da Nada Farfesa Abdullahi Saleh Usman A Matsayin Shugaban Hukumar Hajji Ta Kasa (NAHCON).

aksam

aksam

RelatedPosts

Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, Ya Koma  Jam’iyyar National Democratic Congress (NDC)  A Hukumance; Inda Ya Karɓi Katin Zama Mamba Na Jam’iyyar
SIYASA

Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, Ya Koma Jam’iyyar National Democratic Congress (NDC) A Hukumance; Inda Ya Karɓi Katin Zama Mamba Na Jam’iyyar

by aksam
May 3, 2026
Gwamnatin Jihar Bauchi Ta Umarci  Duk Masu Riƙe Da Mukaman Siyasa Dake Da Niyyar Tsayawa Takara Dasu Yi Murabus Kafin Ranar Juma’a 24 ga Watan Afrilu 2026
SIYASA

Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Mohammed Ya Fice Daga Jam’iyar PDP

by aksam
May 2, 2026
Ba Za Mu Bawa Kwankwaso Tikitin Takarar Shugabancin Kasa A Jam’iyyarmu— NNPP
SIYASA

Wasu Dalilin Da Suka Sa Kwankwaso Ke Shirin Ficewa Daga Jam’iyyar ADC

by aksam
May 2, 2026
Masu Ruwa Da Tsaki A  APCn Kano Sun Amince Da Takarar Abba da Tinubu Karo Na Biyu A Zaɓen 2027
SIYASA

Masu Ruwa Da Tsaki A APCn Kano Sun Amince Da Takarar Abba da Tinubu Karo Na Biyu A Zaɓen 2027

by aksam
May 1, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Προνόμια του VIP Προγράμματος στο polestar casino

April 22, 2025
Abba Atiku Abubakar, Dan Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Alhaji Atiku Abubakar, Ya Sanar Da Ficewarsa Daga Jam’iyyar Da Yake a Baya, Tare Da Shiga Jam’iyyar APC

Abba Atiku Abubakar, Dan Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Alhaji Atiku Abubakar, Ya Sanar Da Ficewarsa Daga Jam’iyyar Da Yake a Baya, Tare Da Shiga Jam’iyyar APC

January 16, 2026
ADVERTISEMENT

Trending.

Mu Na Gayyatar  ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Comr.  Usaini Sani Adamu !!!

Mu Na Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Comr. Usaini Sani Adamu !!!

April 24, 2026
Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Umar SA’ID

Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Umar SA’ID

April 20, 2026
Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

May 4, 2026
Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID

Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID

April 17, 2026
Atiku, Kwankwaso , Obi Sun Jagoranci Zanga-Zanga A Babban Birnin Tarayya Abuja

Atiku, Kwankwaso , Obi Sun Jagoranci Zanga-Zanga A Babban Birnin Tarayya Abuja

April 8, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media