Daga: Hassan Umar Gwammaja
Kwamishinan Matasa da Cigaban Wasanni na Jihar Kano, Mustapha Rabiu Kwankwaso, ya yi murabus daga mukaminsa nan take.
An rawaito cewa Mustapha ɗan jagoran jam’iyyar NNPP, Rabiu Musa Kwankwaso ya tabbatar da murabus ɗin nasa ne ta wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na Facebook a ranar Litinin.
A cikin sanarwar, Mustapha ya bayyana cewa ya yi murabus daga matsayin Kwamishinan Ma’aikatar Matasa da Raya Wasanni, tare da ficewa daga Majalisar Zartarwar Jihar Kano, yana mai cewa ya ɗauki matakin ne cikin jimami.
Sannan ya nuna godiya ga Gwamna Abba Kabir Yusuf bisa damar da ya ba shi na yi wa al’ummar Kano hidima, inda ya ce ya amfana da ƙwarewa da darussa masu yawa a lokacin da yake kan mukamin.
Mustapha ya kuma yi addu’ar ci gaba da bai wa matasan Kano kulawa da goyon baya, tare da fatan shirye-shiryen raya wasanni a jihar za su ci gaba da bunƙasa.
A ƙarshe, ya roƙi Allah Maɗaukakin Sarki Ya ci gaba da albarkar Jihar Kano, tare da yi wa gwamnati da al’ummar jihar fatan alheri.












