Daga Maryam Muhammad Suleiman
JaridarbDaily Trust ta ruwaito cewa wurin da lamarin ya faru iyaka ce tsakanin kananan hukumomin Agaie da Lapai.
Majiyoyi sun shaida wa wakilin Daily Trust cewa, ibtila’in ya faru ne a yau Talata amma ba a samu asarar rai ba.
Wani mazaunin Lapai, Malam Mahmud
Abubakar, ya ce tankar ta fadi kuma ta kone kurmus a lokacin da ta ke kokarin wuce wata babbar mota.
Abubakar ya ci gaba da bayyana cewa wata tankar mai ma ta fashe a daidai wurin a makon da ya gabata.










