Rahotanni daga Karamar Hukuma Takai ya bayyana cewa matakin tsige shugaban Karamar Hukuma ya biyo bayan zarge-zarge da dama da Kansilolin yankin suka gabatar a kansa, ciki har da rashin gudanar da zaman majalisar zartarwa, tin daga lokacin da ya shiga ofishin sa, da rashin iya gudanada mulki da kuma wasu matsaloli da suka shafi tafiyar da harkokin Shugabancin karamar hukumar.
Wasu daga cikin Kansilolin Karamar Hukumar sun ce sun ɗauki wannan mataki ne, domin tabbatar da ingantaccen shugabanci da kuma kare muradun al’ummar yankin.










