Daga: Hassan Umar Gwammaja
A cewar mazauna unguwar, an gina ofishin ne ba bisa ƙa’ida ba, kuma yana hana zirga-zirgar ababen hawa da masu tafiya a ƙafa, musamman saboda yadda yake toshe gani ga masu amfani da hanyar.
Sun kuma yi zargin cewa jami’an da ke aiki a ofishin suna amfani da shi wajen karɓar kuɗaɗe daga masu ababen hawa, lamarin da suka ce ya saɓa da doka.
Mazauna sun tuna cewa a baya jami’an Civil Defence sun taɓa kafa irin wannan ofishi na wucin gadi a kan titin Kurna kusa da gada, amma daga bisani Hukumar KNUPDA ta rusa shi.
A halin yanzu, mazauna yankin sun bayyana damuwa kan sake buɗe irin wannan ofishi a Kofar Mazugal, suna mai cewa yana barazana ga lafiyar masu ababen hawa da sauran masu amfani da hanyar.












