Kungiyar masu kasuwancin kayayyaki Sawa ta mazan kwarai dake kasuwar Kantin kwari anan Kano ta bukaci hukumomi da Gwamnatoci a matakai daban _daban da su tallafawa Kananan yankasuwar domin habaka kasuwancinsu.
Shugaban Kungiyar Alh Usman Sulaiman ne ya bukaci hakan a lokacin da yake zantawa da Manama labarai a ofishin Kungiyar dake kasuwar Kantin kwari.
Shugaban Kungiyar yace akwai bukatar Gwamnatocin su waiwayi Kungiyar musamman Gwamnatin jihar Kano, Yadda take ta aikace -aikace a ciki da wajen jihar Kano,Inda yace yakamata Gwamnatin ta yi duba na tsanaki dangane da kungiyoyin da suke bata gudunmawa a harkokin shugabanci Wanda Kungiyar masu tebura ta mazan kwarai na daya daga cikin kungiyoyin da suke bata hadin Kai a kodayaushe ba tare da ta sani ba.
Usman Sulaiman yace lokaci yayi da Gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin Injiniya Abba Kabir Yusuf za ta tallafawa Kananan yankasuwar da jarin da za su habaka kasuwancinsu domin su ma su sharbi Roman Dimakaradiyya a matsayinsu na asalin Yan jihar Kano.
Shugaban Kungiyar ya kuma bayyana cewar, Kungiyar masu kasuwancin kayayyaki Sawa ta Yan tebura ta yi mutukar ba da gagarumar gudunmawa wajen kafa wannan Gwamnati a lokacin da wasu suka gujeta, a Don haka Kungiyar take Kira ga Gwamnan da babbar Maurya da ya tuna da Kungiyar ‘yantebura ta mazan kwarai dake kasuwar Kantin kwari.
Haka zalika Kungiyar mazan kwarai tana tattarawa Gwamnatin kudaden haraji ta hanyar wayarwa da ‘ya’yanta Kai dangane da kudaden Wanda da sune Gwamnatin take gudanar da ayyukan ci gaba domin alumna su amfana.
Shugaban Kungiyar yace Kungiyar tana taimakawa ‘ya’yanta a duk lokacin da ta ga wani danta ya Shiga wani halin matsin rayuwa Wanda wannan tana yinsa ne ta hanyar yin karo-karo daga manbobinta,saboda hakan ne Kungiyar take bukatar Gwamnatocin su kawo ta su gudunmawar domin ganin ta tallafawa Kananan yankasuwa da Basu da jarin da za su juya su yi kasuwancinsu.
Daga karshe Shugaban Kungiyar ya shawarci yankungiyar da su ci gaba da baiwa Gwamnatin jihar Kano da Kungiyar cikakken hadin Kan daya kamata domin ciyar da alumma da kasuwancinsu da ma ita kanta jihar Kanon gaba.












