Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE) ta ce tana nan daram wajen bin hanyar diflomasiyya da neman mafita cikin lumana a yayin da rikice-rikicen duniya ke ƙaruwa, tare da yin gargaɗi kan manufofin faɗaɗa iko a rikicin Isra’ila da Falasɗinu.
“Yau mun sake tsayawa a gagarumin mataki. Duniya ta cika da rikice-rikice, yaƙe-yaƙe da matsalolin jinƙai. Barazana ga ikon ƙasashe, haɗarin yaduwar makamai da kuma ƙarfafa akidar tsattsauran ra’ayi na ci gaba da lalata tushen zaman lafiya da ci gaba,” in ji Lana Nusseibeh, Ministar Jiha ta UAE, a gaban Babban Taron Majalisar Dinkin Duniya.
Ta ce manufar ƙasarsu “ba wai kawai sarrafa rikice-rikice ba ce, sai dai samar da mafita mai ɗorewa” ta hanyar tattaunawa da sassauci.
“Abin da muke gani a yau a rikicin Falasɗinu da Isra’ila ba wai kawai sakamakon matsaloli bane, amma yana amfanar da ‘yan tsattsauran ra’ayi da masu hura wutar yaƙi waɗanda ke ƙoƙarin tarwatsa hanyar samun zaman lafiya.”












