Daga Hassan Umar Gwammaja
Shugaban Kungiyar Zayyanu Murtala shi ne ya bayyana hakan a zantawar sa da manema labarai a ofishin sa inda yace babu wani batu da ke kama da cewa gwamnatin Kano tana sayar da masallacin idi ga wasu Yankasuwa kamar yadda rade-radin ke cewa
Yace tin bayan rushe gine-ginen da wacce gwamnatin da ta shude ta gudanar suka yi ta fadi tashi a kan Gwamna ya dube su da idon tausyi kasancewar dama can sune suke gudanar da harkokin kasuwanci a gurin fiye da shekara 25 amma aka tashe su ba tare da samar musu da wani matsugunin ba.
A cewar sa wannan gwamnatin ta ji kukan su ta dawo musu da shi kuma ta basu shedar zama a gurin.
Shima shugaban iyayen kungiyar Malam Yakubu Tijani yace babu wani abu dake kama da ana sayar da gurin sai dai yarfe Kawai na siyasa da yan adawa ke yi wa gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf kuma insha Allah ba za su yi nasara ba
A nasa jawabin tsohon sakataren kungiyar Misbahu Musa Fage ya ja hankalin mazauna gurin da su kwantar da hankalin su babu ko shakka Gwamna yana San talakawa Kano kuma ba zai yi abin da zai cutar da su ba.












