Kungiyar yankasuwa dake tashar motoci ta malam Kato ta jaddada aniyarta na ci gaba da baiwa Gwamnatin jihar Kano hadin Kai domin tattara kudaden haraji domin ciyar da Jihar Kano gaba.
Shugaban Kungiyar Abdullahi Adamu ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da Manema labarai a ofishinsa dake tashar Malam Kato.
Shugaban Kungiyar yace yankasuwar da suke gudanar da kasuwanci a cikin tashar mutane ne masu biyayya da hadin Kai, musamman duk abubuwan da suka shafi al’ummar jihar Kano basa yin kasa a gwiwa saboda abune da zai taimakawa jama’a da samarwa matasa ayyukan yi.
Shugaban Kungiyar yayi Kira ga Gwamnatin jihar Kano da ta tallafawa tashar motoci ta malam Kato da futulu masu amfani da gaske rana a ciki da wajen tashar saboda Samar da tsaro na dukiyoyin alumma.
Bugu da Kari akwai bukatu da dama da ya kamata Gwamnatin jihar Kano ta yi a cikin tashar Malam Kato saboda ta yiwa al’ummar tashar kadan saboda gine -gine da aka yi a cikinta, Inda yace akwai bukatar Gwamnati ta kawowa tashar daukin gaggawa.
Shugaban Kungiyar ya Kara da cewar,a shirye Kungiyar take na ganin ta ci gaba da baiwa Gwamnatin jihar gudunmawa da ta dace, domin marawa yunkuri Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf bisa Yadda yake aiwatar da ayyukan ci gaba a fadin jihar.
Daga karshe Shugaban Kungiyar yayi Kira ga dukkannin ‘ya’yan Kungiyarsa da su kwantar da hankalunsu domin Yanzu haka shugabancin Kungiyar Yana nan nemowa ‘ya’yan Kungiyar tallafi na musamman da za su habaka kasuwancinsu.
Yace amma dole ne sai sun ci gaba da baiwa Gwamnatin jihar Kano goyan bayan da suka dace, saboda Gwamnatin ta samu damar taimaka musu karkashin ma’aikatar kasuwanci ta jihar Kano.









