• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Yadda Kotu taci tarar CBN Naira miliyan 63.7

aksam by aksam
February 23, 2024
Reading Time: 2 mins read
0
Home LABARAI
ADVERTISEMENT
467
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta umurci babban bankin Najeriya CBN ya biya wani Bajamushe, Martin Gegenheimer Naira miliyan 63.7 da dala 10,000 bisa kama shi da tsare shi da hukumar kula da shige da fice ta Najeriya NIS ta yi ba bisa ka’ida ba.

A wani hukunci da ya yanke a ranar Alhamis, Mai shari’a Inyang Ekwo, ya umarci babban bankin kasar CBN, da ya cire kudaden daga asusun gwamnatin tarayya da ke hannun ta, domin daidaita bashin da ya taso daga hukuncin 2021 da kotun alkalai ta kasashen yammacin Afrika ECOWAS ta yankewa Najeriya.

RelatedPosts

Wani Matashi Ya Rasu A Gidan Budurwarsa ƴar Tik-tok Dake Unguwar Ɗanbare A Jihar Kano

Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro

Sky News: Yaƙin Trump da Iran Na Daya Daga Cikin Manyan Kurakuran Dabarun Amurka

Mai shari’a Ekwo ya yi watsi da bayanin CBN cewa, a halin yanzu asusun gwamnatin tarayya na cikin gibi, wanda hakan ya sa ba za a iya biyan dukkan kudaden hukuncin ba.

Bajamushen, wanda ya ce ya ziyarci Najeriya ne a wata ziyarar aiki, ya bayyana cewa, yayin da yake komawa Kenya a ranar 23 ga watan Fabrairun 2020, jami’an hukumar kula da shige da fice ta Najeriya sun tare shi a kofar shiga jirgin saman Kenya Airways bayan an kammala dukkan ka’idojin tashin jirgi.

Ya ce jami’an NIS sun kama shi, suka kwace fasfo dinsa tare da tsare shi a wani dakin da ke da cunkuso daga 23 ga Fabrairu, 2020 zuwa 4 ga Maris, 2020, duk da cewa akwai ka’idojin cutar COVID-19 da ya kamata a kula.

A karshe dai ya kalubalanci kama shi da tsare shin da aka yi a gaban Kotun ECOWAS.

A cikin hukuncin ranar 4 ga Maris, 2021, wani kwamitin mutane uku na kotun , karkashin jagorancin shugaban kotun, Mai shari’a Edward Amoako Asante, ya bayyana kama Gegenheimer da tsare shi da aka yi a matsayin ba bisa ka’ida ba.

Kotun ta umurci gwamnatin Najeriya da ta biya shi N53,650,925 a matsayin diyya na musamman kan hasarar da ya samu da kuma kashe-kashen kudaden da ya yi a lokacin da hukumar NIS ke tsare da shi ba bisa ka’ida ba.

Kotun ta kuma umurci gwamnatin Najeriya da ta sake biyansa diyyar Naira miliyan 10 a matsayin diyya ga duk wani laifi da rashin adalci da aka yi masa na tauye masa hakkinsa, sannan kuma karin dala 10,000 da ya kashe yayin da yake neman beli.

Kotun ta ECOWAS dai ta umarci gwamnatin Najeriya da ta cire Bajamushen daga jerin sunayen da take sa ido, sannan ta gaggauta sakin fasfo dinsa na Jamus ba tare da wani sharadi ba, wanda jami’an gwamnatin Najeriya suka kwace ba bisa ka’ida ba.

Share187Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Cigaba da bullar almundahna, majalisar dattawa ta jaddada Aniyar ta na bincikar gwamnatin Buhari

Next Post

Gawurtaccen danfashin daji ya hadu da ajalinsa a hanun jamian tsaro

aksam

aksam

RelatedPosts

Wani Matashi Ya Rasu A Gidan Budurwarsa  ƴar Tik-tok  Dake Unguwar  Ɗanbare A Jihar Kano
LABARAI

Wani Matashi Ya Rasu A Gidan Budurwarsa ƴar Tik-tok Dake Unguwar Ɗanbare A Jihar Kano

by aksam
June 20, 2026
Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro
LABARAI

Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro

by Khadija Maitaya
June 19, 2026
Sky News: Yaƙin Trump da Iran Na Daya Daga Cikin Manyan Kurakuran Dabarun Amurka
LABARAI

Sky News: Yaƙin Trump da Iran Na Daya Daga Cikin Manyan Kurakuran Dabarun Amurka

by Khadija Maitaya
June 16, 2026
China Ta Soke Darussa 12,000 na Jami’o’i Domin Shirin Zamani na AI
LABARAI

China Ta Soke Darussa 12,000 na Jami’o’i Domin Shirin Zamani na AI

by Khadija Maitaya
June 14, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Majalisar Dokoki ta nemi sanata Abdul Ningi ya dawo bakin aiki

Majalisar Dokoki ta nemi sanata Abdul Ningi ya dawo bakin aiki

May 28, 2024

Bayan bude bodojin Najeriya, kasar Niger ta rufe iyakokin ta da Najeriya

March 17, 2024
ADVERTISEMENT

Trending.

Mu Na Gayyatar  ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Ango Bulaye

Mu Na Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Ango Bulaye

June 12, 2026
An Kammala Gasar Kwallon Kafar Sada Zumunchi Dan Muna Murnar Zagayuwar Sallah Babba Cikin Nasara A Garin Nkawkawo Dake Kasar Ghana

An Kammala Gasar Kwallon Kafar Sada Zumunchi Dan Muna Murnar Zagayuwar Sallah Babba Cikin Nasara A Garin Nkawkawo Dake Kasar Ghana

June 1, 2026
The Emir of Zangon Nkawkawo, Alhaji Abdul-Nasir Usman, Extends Eid Greetings

The Emir of Zangon Nkawkawo, Alhaji Abdul-Nasir Usman, Extends Eid Greetings

June 1, 2026
Irin Yadda Ake Cigaba Da Gudanar Da  Karatun Saukar Al’qur’ani Mai Girma  A Zango Nkawkawo Dake Kasar Ghana

Irin Yadda Ake Cigaba Da Gudanar Da Karatun Saukar Al’qur’ani Mai Girma A Zango Nkawkawo Dake Kasar Ghana

June 5, 2026
Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Sha’ibu Sani Mai Atamfa (Bulaye)

Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Sha’ibu Sani Mai Atamfa (Bulaye)

June 15, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media