Kungiyar injiniyoyi ta kasa shiyar Arewa maso yamma ta jaddada aniyarta na Kula da ingancin ayyukan da injiniyoyi suke gudanarwa a fadin kasar nan.
Shugaban Kungiyar na kasa Eng. Farfesa Sadiq Abubakar ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da Manema labarai a yayin kaddamar da sabbin Shugabannin Kungiyar Wanda ya gudana a dakin taro na dangote dake jami’ar Bayero a nan Kano.
Injiniya Sadiq Abubakar yace saboda yawan matsalolin da Ake samu wajen yin gine -gine a fadin kasar nan,ya sanya Kungiyar ta ga dacewar Samar da jagororin da su rika bibiyar Yadda Injiniyoyi suke aiwatar da ayyukan su.
Shugaban yace akwai bukatar cibiyar ta rika bibiyar dukkannin ayyukan da ‘ya’yanta suke yi ta hanyar wadan nan sabbin Shugabannin da aka kaddamar na jihohin Arewa maso yamma saboda yawan karafe korafen da samu a harkokin gine -gine.
A jawabinsa Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf Wanda kwamashin ayyuka na jihar Kano Alh Marwan Ahmed ya wakilta yace Gwamnatin jihar Kano ta yi farin ciki da wannan sabbin Shugabanni saboda za su taimaka Mata wajen aiwatar ayyukanta domin tabbatar da ingancin ayyukan da yankwangila suke yi a jihar duba da managartan ayyukan da yi a lunguna da sako na na wannan jiha.
Yace rashin irin wadannan jagorori ya sanya wasu kamfanoni kwangila suke abun da suka ga dama saboda sun fahinci babu wadanda suke bibiyar dukkannin ayyukan hanyoyi da gine -gine da suke gudanarwa a shiyar Arewa maso yamma.
Kwamishinan ya bayyana cewar, Kungiyar injiniyoyi ta kasa ba za ta zuba idanu ba tana kallon irin matsaloli na gudanar da ayyuka marasa inganci su rika faruwa a cikin jihar Wanda ita dukkannin ayyukan da take aiwatarwa ayyuka ne masu mutukar nagarta.
Daga karshe kwamishinan ya yabawa shugabancin Kungiyar na kasa bisa dogon tunani da ta yi na Samar da sabbin Shugabannin wadanda a baya babu su, Inda yace hakan zai Kara habakawa da tabbatar da ingancin ayyukan da ake yi a yankunan Arewacin kasar nan.












