• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Kalli yadda wasu masu garkuwa da mutane suka hadu da ajalin su a kokarin sace wasu mutane

Sy lawan by Sy lawan
January 26, 2024
Reading Time: 2 mins read
0
Home LABARAI
ADVERTISEMENT
466
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Wasu miyagun ƴan bindiga 3 da suka kware wajen garkuwa da mutane sun baƙunci lahira.

Lamarin ya faru ne a jihar Adamawa da ke shiyyar Arewa maso Gabashin Najeriya.

RelatedPosts

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Ya Sanya Ranar Talata 05 GA watan Mayu 2026, A Matsayin Ranar Da Zai Jagoranci Rantsar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

NDLEA Ta Kama Mutane 6, Ta Rushe Maboyar Miyagun Kwayoyi a BUK Old Site Kano

Jaridar The Nation ta bankado cewa dakarun ƴan sanda ne suka sheƙe su a wani samame da suka kai tare da taimakon mafarauta ƴan sa’kai.

Yayin wannan samame da jami’an tsaron suka fita, sun yi nasarar ceto mutum biyu da ƴan bindigan suka yi garkuwa da su, Daily Post ta ruwaito.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ƴan sandan jihar Adamawa, SP Suleiman Nguroje, ne ya tabbatar da haka a wata sanarwa ranar Alhamis, 25 ga watan Janairu.

Ya ce ranar Laraba, 24 ga watan Janairu, 2024, ‘yan sanda suka ragargaji kungiyar miyagun a tsaunin Koma mai hade da garuruwan Kojoli da Karlahi na kananan hukumomin Jada da Fufore a Adamawa.

Yan sanda sun ceto mutum da aka sace Kakakin ƴan sandan ya ci gaba da cewa:

“Jiya Laraba, masu garkuwa suka kai hari a wani wurin kiwon shanu na Alhaji Jibo Karlahi inda suka tafi da Umar Jibo mai shekaru 18 da Idi Hassan mai shekaru 13 a duniya.

“Nan take rundunar ƴan sanda ta tashi tawagar ceto suka bi sawun maharan.

Daga ganin dakarunmu sai suka buɗe wuta aka fara musayar wuta. Sakamakon haka muka kashe 3 daga cikinsu.

“Amma sauran sun ari na kare ɗauke da raunukan harbin bindiga, abin farin cikin mun yi nasarar ceto mutum 2 da suka sato ba tare da an cutar da su ba.

” A cewarsa, wannan nasara na ɗaya daga cikin ƙoƙarin rundunar na magance aikata manyan laifuka da suka haɗa da garkuwa, satar shanu, fashi da sauransu a jihar.

Share186Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Kurakurai biyar da Tinibu ya gaza bayar da gamsar su ga Turakin Adamawa, Atiku Abubakar

Next Post

Rikicin kabilanci da Addini na kara kamari a jihar pilato

Sy lawan

Sy lawan

RelatedPosts

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Ya Sanya Ranar Talata 05 GA watan Mayu 2026, A Matsayin Ranar Da Zai Jagoranci Rantsar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan
LABARAI

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Ya Sanya Ranar Talata 05 GA watan Mayu 2026, A Matsayin Ranar Da Zai Jagoranci Rantsar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan

by aksam
May 4, 2026
Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano
LABARAI

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

by aksam
May 4, 2026
NDLEA Ta Kama Mutane 6, Ta Rushe Maboyar Miyagun Kwayoyi a BUK Old Site Kano
LABARAI

NDLEA Ta Kama Mutane 6, Ta Rushe Maboyar Miyagun Kwayoyi a BUK Old Site Kano

by Khadija Maitaya
May 4, 2026
Tsohon Dan Takarar Shugaban Kasa A  Jam’iyyar Labour Party, Peter Obi, Ya Sanar Da Ficewarsa Daga  Jam’iyyar Haɗaka Ya ADC
LABARAI

Tsohon Dan Takarar Shugaban Kasa A Jam’iyyar Labour Party, Peter Obi, Ya Sanar Da Ficewarsa Daga Jam’iyyar Haɗaka Ya ADC

by aksam
May 3, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Tinibu zai ciyo bashin Dala Biliyan guda dan cike gurbin kasafin 2024

Tinibu zai ciyo bashin Dala Biliyan guda dan cike gurbin kasafin 2024

November 29, 2023
Matsin Rayuwa:- Yasa Wani Magidanci Ya Cire Rufin Kwanon Masallacin Da Ya Gina Shekaru 30 Da Suka Wuce Domin Ya Siyar Kayan Abinci

Matsin Rayuwa:- Yasa Wani Magidanci Ya Cire Rufin Kwanon Masallacin Da Ya Gina Shekaru 30 Da Suka Wuce Domin Ya Siyar Kayan Abinci

February 20, 2024
ADVERTISEMENT

Trending.

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

May 4, 2026
Mu Na Gayyatar  ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Comr.  Usaini Sani Adamu !!!

Mu Na Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Comr. Usaini Sani Adamu !!!

April 24, 2026
Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Umar SA’ID

Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Umar SA’ID

April 20, 2026
Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID

Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID

April 17, 2026
Atiku, Kwankwaso , Obi Sun Jagoranci Zanga-Zanga A Babban Birnin Tarayya Abuja

Atiku, Kwankwaso , Obi Sun Jagoranci Zanga-Zanga A Babban Birnin Tarayya Abuja

April 8, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media