DAGA HASSAN UMAR GWAMMAJA
Al’amarin ya faru ne a Birnin Kudu dake jihar Jigawa, lamarin da ya razana al’umma.
Shi dai wannan bawan Allah wanda aka sakaya sunansa shi ne ainihin wanda ya gina Masallacin tsawon shekaru talatin da suka shuɗe, sai yanayin matsin rayuwa tasa ya ga ya dace ya gina shaguna a wani ragowar filin harabar Masallacin, lamarin da mutane sukace basu san wannan ba, tunda ya riga ya gina Masallacin ya barwa al’umma.
Dalilin haka ya fusata ya hau ya fara cire rufin kwanon Masallacin da zummar ya fasa yin Masallaci.












