• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Cikin wata shidan 2025 yan ta’adda sun kashe mutane fiye da na shekarar 2024: bayanin ya tabbatar

aksam by aksam
July 9, 2025
Reading Time: 1 min read
0
Home Uncategorized
ADVERTISEMENT
466
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Alkaluman da Hukumar Kare Hakkokin Dan’adam ta Nijeriya ta fitar sun bayyana cewa a watanni shida na farkon 2025, ‘yan ta’adda da ‘yan bindiga sun kashe a kalla mutum 2,266 a kasar.

Wannan adadi ya zarta na watanni shidan farko na 2024 inda aka kashe mutum 1,083, sannan a shekarar gaba daya kuma suka kashe jimillar 2,194.

RelatedPosts

Halifatul Akabar Sheikh Ahmad Abdullah Mai Kano Jallo Ya Halarci Mulundin Garin Zangon Nkawkawo

Irin Yadda Aka Gudanar Da Zagayen Mauludn Tunawa Ga Ranar Da Aka Haifi Annabi Muhammadu SWA A Garin Nkawkawo

Kasar Ghana Ta Bayyana Shirinta Na ƙara Samar Da Wutar Lantarki Domin Sayarwa Najeriya Da Sauran ƙasashen Yammacin Afirka

Sojojin Nijeriya na yaƙi da ‘yan ta’addar Boko Haram a arewa maso-gabas da ‘yan bindiga da garkuwa da mutane a arewa maso-yamma, da ƙoƙarin daƙile hare-haren makiyaya a tsakiyar kasar da kuma ‘yan-a-ware a kudu maso gabashin kasar.

Lamarin ya ta’azzara a baya bayan nan, inda a watan da ya gabata kadai aka kashe mutum 606, ciki har da harin ‘yan bindiga a yankunan Yelewata da Dauda na jihar Benue inda aka kashe mutum 200.

Sakataren Zartarwa na Hukumar Kare Hakkokin Dan’adam ta Kasa Tony Ojukhu, ya bayyana alkaluman a yayin wani taro a Abuja, inda ya yi kira da a dauki matakan da suka kamata daga bangaren gwamnati.

“Wadannan ba alkaluma ne na rahotanni kawai ba; ana maganar iyaye maza da mata, yara kanana, da ‘yan’uwa da dangi da aka ɗaidaita, aka lalata jin dadin rayuwarsu, sannan aka dusashe hasken makomarsu ta mummunar hanya,” in ji Ojukwu.

Hukumar ta kuma bayar da rahoton cewa an yi garkuwa da mutum 857 a watanni shida na farkon 2025, duk da cewa an samu ragi idan aka akwatanta da mutum 1,461 da aka yi garkuwar da su a watanni shidan farko na 2024.

Kazalika, rahoton ya lura da yadda ake kai hare-hare kan jami’an tsaro da ‘yan sintiri na yankuna, inda aka kashe sojoji sama 17 a jihohin Kaduna da Neja, da mambobin ‘yan bijilante fiye 40 a jihar Zamfara ta arewa maso-yamma.

Share186Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Yadda kotu ta yanke hukuncin shekaru 8654 ga wani Danjarida

Next Post

Taron Masu Auren Jinsi, Ƙasar Senegal ta gargadi MDD

aksam

aksam

RelatedPosts

Halifatul Akabar Sheikh Ahmad Abdullah Mai Kano Jallo Ya Halarci Mulundin Garin Zangon Nkawkawo
Uncategorized

Halifatul Akabar Sheikh Ahmad Abdullah Mai Kano Jallo Ya Halarci Mulundin Garin Zangon Nkawkawo

by aksam
September 5, 2026
Irin Yadda Aka Gudanar Da Zagayen Mauludn Tunawa Ga Ranar Da Aka Haifi  Annabi Muhammadu SWA  A Garin Nkawkawo
Uncategorized

Irin Yadda Aka Gudanar Da Zagayen Mauludn Tunawa Ga Ranar Da Aka Haifi Annabi Muhammadu SWA A Garin Nkawkawo

by aksam
September 1, 2026
Kasar Ghana Ta Bayyana Shirinta Na ƙara Samar Da Wutar Lantarki Domin Sayarwa Najeriya Da Sauran ƙasashen Yammacin Afirka
Uncategorized

Kasar Ghana Ta Bayyana Shirinta Na ƙara Samar Da Wutar Lantarki Domin Sayarwa Najeriya Da Sauran ƙasashen Yammacin Afirka

by aksam
August 26, 2026
Hukumar Kashe Gobara Ta Jihar Kano Ta Dakile Wata Gobara A Rano
Uncategorized

Hukumar Kashe Gobara Ta Jihar Kano Ta Dakile Wata Gobara A Rano

by aksam
August 26, 2026

Comments 0

  1. ww88 c says:
    1 year ago

    Bài này phân tích cực kỳ sắc bén, đọc xong muốn vào chiến ngay luôn! App mình đang gắn bó gần đây là ww88 c, game đa dạng, chơi hoài không chán.

    Reply

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Gwamnatin tarayya ta ba matatar Mai ta Dangote wata babbar jinga a kasar nan

October 9, 2024

Bayan yanke hukuncin kano Zamfara pilato bangaren sharia ya fara farfado da kimar sa: wani babban lauya

January 14, 2024
ADVERTISEMENT

Trending.

Masu Siye Da Siyar Da Filaye A  R/zakara Sunkoka Da Aibantasu Da Gwamnatin Kano Keyi.

Masu Siye Da Siyar Da Filaye A  R/zakara Sunkoka Da Aibantasu Da Gwamnatin Kano Keyi.

August 26, 2026
Cristiano Ronaldo Ya Auri Georgina Rodríguez

Cristiano Ronaldo Ya Auri Georgina Rodríguez

August 12, 2026
Wani Kauran Mata Ya Jikkata Wata Dattijuwa Bayan Ta Hana Shi Shiga Gurin Da Bai kamata Ba

Wani Kauran Mata Ya Jikkata Wata Dattijuwa Bayan Ta Hana Shi Shiga Gurin Da Bai kamata Ba

August 29, 2026
Masu Zuba Jari 40+ daga Masar na Sha’awar Zuba Jari A Najeriya

Masu Zuba Jari 40+ daga Masar na Sha’awar Zuba Jari A Najeriya

August 23, 2026
Iran Ta Kakkabo Wasu Manyan Jiragen Yaƙi Na Amurka

Iran Ta Kakkabo Wasu Manyan Jiragen Yaƙi Na Amurka

August 14, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media