Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araqchi, ya jaddada bukatar kasashen duniya su dauki matsaya mai nauyi dangane da hare-haren da Amurka da Isra’ila suka kai kan Iran, tare da bukatar a hukunta wadanda suka kaddamar da harin.
A wata tattaunawar waya da ya yi da takwaransa na Jamus, Johann Wadephul, a ranar Juma’a, Araqchi ya yi bayani kan sabbin ci gaban da suka shafi hare-haren soji da Amurka da gwamnatin Isra’ila suka kaddamar kan Iran.
Ya nanata muhimmancin dukkan kasashe su dauki matsayi mai alhaki domin kare dokokin kasa da kasa da kuma ka’idojin kundin tsarin Majalisar Dinkin Duniya.
Yana mai tunatar da yadda Amurka ta saba karya alkawurra akai-akai da kuma laifuffukan da aka aikata a yakin da aka tilasta biyu a cikin shekarar da ta gabata, Araqchi ya bayyana cewa amincewar Jamhuriyar Musulunci ta Iran da tsagaita wuta wata mataki ce mai muhimmanci domin kawo karshen yakin gaba daya, da kuma neman diyya ga barnar da aka yi wa Iran, tare da hukunta masu kai harin. Ya kara da cewa wannan mataki ya dace a yaba masa daga dukkan bangarori.
A yayin tattaunawar, ministan harkokin wajen Jamus ya nuna goyon baya ga dakatar da yakin, tare da jaddada bukatar kawo karshen hare-haren Isra’ila a Lebanon.
Wadephul ya kuma bayyana fatan cewa tattaunawar da ake shirin yi tsakanin tawagogin Iran da Amurka a Islamabad, Pakistan, za ta haifar da dawowar zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.








